Ranakun 6 da 9 ga watan Agusta ranaku ne na tunawa da cika shekaru 81 da aka jefa boma-boman nukiliya a Hiroshima da Nagasaki na Japan. A daidai lokacin da ya kamata Japan ta yi tuba sosai kan laifinta na kai wa wasu kasashe hare-hare da kuma tsamo darasi daga yaki, wani labari da kafafen yada labarai na kasar suka bayar ya tayar da hankalin al’ummar duniya, watau ma’aikatar tsaro ta Japan tana shirin gabatar da kasafin kudin tsaro na shekarar 2027 wanda zai kai Yen tiriliyan 8.9, adadin da ya kai matsayin koli a tarihi.
Kuma saboda akwai dimbin ayyuka da ba a bayyana takamaiman adadin kudinsu ba a cikin kasafin, mai yiyuwa ne a karshe yawan kudin zai kai Yen tiriliyan 10. Yadda yawan kudin ya kai sabon matsayi, ya kara fayyace yunkurin ‘yan siyasar Japan na keta kundin tsarin mulkin zaman lafiya da kuma makircin kasar na farfado da “sabon ra’ayin karfin soja”.
Game da wannan yunkuri mai hadari na gwamnatin Japan, kasashe makwabta sun ci gaba da yin Allah wadai. Tun a farkon wannan shekara, bangaren Sin ya kara tsaurara matakan kayyade fitar da kayayyakin da ake iya amfani da su domin ayyukan farar hula da na soji zuwa Japan, inda ya sanya kamfanonin soja na Japan da dama a cikin jerin wadanda aka kayyade fitarwa kayayyaki tare da sa musu ido, da nufin dakile yunkurin Japan na “sake farfado da karfin soja” da kuma neman mallakar makaman nukiliya. Rasha ma ta yi Allah wadai da yunkurin Japan na “sake farfado da karfin soja” da ke dagula yanayin tsaron yankin da ma duniya.
A nata bangare, Koriya ta Arewa ta yi gargadin cewa, idan Japan ta sami karfin kai hari kafin wasu, to dan Adam zai sake fuskantar bala’i da barazana, kuma sam “ba za a yarda Japan ta zama babbar kasa a bangaren karfin soja ba.”(Amina Xu)














