A baya-bayan nan, wasu karin shugabannin kasashen duniya da na kungiyoyin kasa da kasa sun mika sakon fatan alheri ga shugaban kasar Sin Xi Jinping, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, inda suka taya Sinawa murnar sabuwar shekarar doki.
Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya wallafa sako a shafin sada zumunta, inda ya taya murnar bikin bazara tare da bayyana fatan shekarar doki za ta sanya sabon kuzari ga dangantakar da ke tsakanin Jamus da Sin.
Shugaban Pakistan Asif Ali Zardari ya bayyana kwarin gwiwar cewa Pakistan da Sin za su bude wani sabon babi na hadin gwiwa na kut-da-kut a nan gaba.
Shugabar kwamitin shirya wasannin Olympics na kasa da kasa Kirsty Coventry ta bayyana cewa, bajintar da ’yan wasan kasar Sin suke yi a gasar wasannin Olympics ta lokacin huntutu da ake yi a kasar Italiya, ta sanya matukar alfahari da farin ciki ga jama’ar kasar Sin na gida da waje, lamarin da ya sa bikin ya kara bayar da ma’ana.
Kazalika, sauran wadanda suka aike da sakon taya murna ga shugaba Xi sun hada da: Shugaban Jamhuriyar Demokuradiyyar Kongo Felix Tshisekedi, da shugaban kasar Gambia Adama Barrow, da shugaban gwamnatin rikon kwarya ta Mali Assimi Goita da dai sauransu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post