ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Masu Garkuwa Ne 12 Da Wasu 83 A Jihar Ondo

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
Ondo

Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wadda aka fi sani da Amotekun Corps, ta kama akalla mutane 95 da ake zargin aikata laifuka a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

A cewar rundunar, kama wadannan mutane ya samu ne ta hanyar hadin gwiwa da jami’an ofishin rundunar ‘yan sanda na jihar, Nigeria Security and Civil Defence Corps, Department of State Services, da kuma sojojin Nijeriya.

  • Darussa Daga Ramadan Na (2)
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Kwamandan Amotekun na jihar, Akogun Adeleye, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Kwamandan ya ce wadanda aka kama ana zargin su da aikata laifuka kamar satar mutane (kidnapping), sata, fashi da makami, da kuma hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Ya bayyana wasu daga cikin wadanda ake zargin kamar haka: Bictor, mai shekara 31; Jonathan, mai shekara 34; Akpan, mai shekara 35; Aliu, mai shekara 27; Sanni, mai shekara 20; Adeoye, mai shekara 44; Ayodeji, mai shekara 50; Abdullahi, mai shekara 24; Doman, mai shekara 25; Isaac, mai shekara 20; Peter, mai shekara 25; da Dada, mai shekara 42.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Adeleye ya ce, “A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman Amotekun, ’yansanda, hukumar farin kaya, da DSS, sun yi kokari matuka wajen bibiyar wadanda ake zargi, kuma hakan ya haifar da sakamako mai kyau sosai.”

“Mutum 61 da aka samu a cikin motar tirela, ana zargin su ne, kuma muna ci gaba da tantance su domin sanin matakin da za a dauka bayan an gama tantance su.

“Muna da mutum 19 da suka karya dokar jihar. Muna da uku da suka shafi rikicin harbin shanu tsakanin manoma da makiyaya, sannan muna da 12 da suka shafi satar mutane.

“Labarin mai dadi shi ne cewa wasu daga cikin wadanda ake zargin satar mutane an kama su ne a Karamar Hukumar Akure ta Arewa mai rikici, kuma muna da yakinin cewa wannan zai kawo zaman lafiya a yankin, musamman da ake gudanar da hadin gwiwar ayyukan tsaro a halin yanzu.”

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin satar mutane a wurare kamar Ilu-Abo, Akure; Idogun-Ugbe; yankin Alagbaka; Ayede, Akure; Iloro Camp; da Ogbese a Karamar Hukumar ta Akure Arewa.

“Dangane da rikicin harbin shanu, muna da Umai Jibril da Hassan. Wannan ya kawo jimillar wadanda ake gabatarwa a nan kan wadannan laifuka zuwa 34, yayin da wadanda ba a gabatar da su ba, wadanda ake bincike a kansu a halin yanzu, suna 61.

“Ina so in rubuta a tarihi cewa mun sami nasarar cimma wannan sakamakon ne ta hanyar hadin gwiwar dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman ’yan sanda, NSCDC, DSS, da Rundunar Sojin Nijeriya,” in ji shi.

Adeleye ya gargadi masu laifi da su daina aikata laifuffukansu ko kuma su fuskanci mataki mai tsanani daga hukumomin tsaro.

“Jihar Ondo ba wurin tsira bane ga masu laifi. Za mu ci gaba da hadin gwiwa da hukumomi masu alaka domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi,” in ji Kwamandan Amotekun.

Ondo
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Ondo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.