ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Masu Garkuwa Ne 12 Da Wasu 83 A Jihar Ondo

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
Ondo

Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wadda aka fi sani da Amotekun Corps, ta kama akalla mutane 95 da ake zargin aikata laifuka a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

A cewar rundunar, kama wadannan mutane ya samu ne ta hanyar hadin gwiwa da jami’an ofishin rundunar ‘yan sanda na jihar, Nigeria Security and Civil Defence Corps, Department of State Services, da kuma sojojin Nijeriya.

  • Darussa Daga Ramadan Na (2)
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Kwamandan Amotekun na jihar, Akogun Adeleye, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Kwamandan ya ce wadanda aka kama ana zargin su da aikata laifuka kamar satar mutane (kidnapping), sata, fashi da makami, da kuma hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Ya bayyana wasu daga cikin wadanda ake zargin kamar haka: Bictor, mai shekara 31; Jonathan, mai shekara 34; Akpan, mai shekara 35; Aliu, mai shekara 27; Sanni, mai shekara 20; Adeoye, mai shekara 44; Ayodeji, mai shekara 50; Abdullahi, mai shekara 24; Doman, mai shekara 25; Isaac, mai shekara 20; Peter, mai shekara 25; da Dada, mai shekara 42.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Adeleye ya ce, “A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman Amotekun, ’yansanda, hukumar farin kaya, da DSS, sun yi kokari matuka wajen bibiyar wadanda ake zargi, kuma hakan ya haifar da sakamako mai kyau sosai.”

“Mutum 61 da aka samu a cikin motar tirela, ana zargin su ne, kuma muna ci gaba da tantance su domin sanin matakin da za a dauka bayan an gama tantance su.

“Muna da mutum 19 da suka karya dokar jihar. Muna da uku da suka shafi rikicin harbin shanu tsakanin manoma da makiyaya, sannan muna da 12 da suka shafi satar mutane.

“Labarin mai dadi shi ne cewa wasu daga cikin wadanda ake zargin satar mutane an kama su ne a Karamar Hukumar Akure ta Arewa mai rikici, kuma muna da yakinin cewa wannan zai kawo zaman lafiya a yankin, musamman da ake gudanar da hadin gwiwar ayyukan tsaro a halin yanzu.”

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin satar mutane a wurare kamar Ilu-Abo, Akure; Idogun-Ugbe; yankin Alagbaka; Ayede, Akure; Iloro Camp; da Ogbese a Karamar Hukumar ta Akure Arewa.

“Dangane da rikicin harbin shanu, muna da Umai Jibril da Hassan. Wannan ya kawo jimillar wadanda ake gabatarwa a nan kan wadannan laifuka zuwa 34, yayin da wadanda ba a gabatar da su ba, wadanda ake bincike a kansu a halin yanzu, suna 61.

“Ina so in rubuta a tarihi cewa mun sami nasarar cimma wannan sakamakon ne ta hanyar hadin gwiwar dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman ’yan sanda, NSCDC, DSS, da Rundunar Sojin Nijeriya,” in ji shi.

Adeleye ya gargadi masu laifi da su daina aikata laifuffukansu ko kuma su fuskanci mataki mai tsanani daga hukumomin tsaro.

“Jihar Ondo ba wurin tsira bane ga masu laifi. Za mu ci gaba da hadin gwiwa da hukumomi masu alaka domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi,” in ji Kwamandan Amotekun.

Ondo
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Ondo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.