ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Masu Garkuwa Ne 12 Da Wasu 83 A Jihar Ondo

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 months ago
Ondo

Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wadda aka fi sani da Amotekun Corps, ta kama akalla mutane 95 da ake zargin aikata laifuka a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

A cewar rundunar, kama wadannan mutane ya samu ne ta hanyar hadin gwiwa da jami’an ofishin rundunar ‘yan sanda na jihar, Nigeria Security and Civil Defence Corps, Department of State Services, da kuma sojojin Nijeriya.

  • Darussa Daga Ramadan Na (2)
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Kwamandan Amotekun na jihar, Akogun Adeleye, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Kwamandan ya ce wadanda aka kama ana zargin su da aikata laifuka kamar satar mutane (kidnapping), sata, fashi da makami, da kuma hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Ya bayyana wasu daga cikin wadanda ake zargin kamar haka: Bictor, mai shekara 31; Jonathan, mai shekara 34; Akpan, mai shekara 35; Aliu, mai shekara 27; Sanni, mai shekara 20; Adeoye, mai shekara 44; Ayodeji, mai shekara 50; Abdullahi, mai shekara 24; Doman, mai shekara 25; Isaac, mai shekara 20; Peter, mai shekara 25; da Dada, mai shekara 42.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Adeleye ya ce, “A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman Amotekun, ’yansanda, hukumar farin kaya, da DSS, sun yi kokari matuka wajen bibiyar wadanda ake zargi, kuma hakan ya haifar da sakamako mai kyau sosai.”

“Mutum 61 da aka samu a cikin motar tirela, ana zargin su ne, kuma muna ci gaba da tantance su domin sanin matakin da za a dauka bayan an gama tantance su.

“Muna da mutum 19 da suka karya dokar jihar. Muna da uku da suka shafi rikicin harbin shanu tsakanin manoma da makiyaya, sannan muna da 12 da suka shafi satar mutane.

“Labarin mai dadi shi ne cewa wasu daga cikin wadanda ake zargin satar mutane an kama su ne a Karamar Hukumar Akure ta Arewa mai rikici, kuma muna da yakinin cewa wannan zai kawo zaman lafiya a yankin, musamman da ake gudanar da hadin gwiwar ayyukan tsaro a halin yanzu.”

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin satar mutane a wurare kamar Ilu-Abo, Akure; Idogun-Ugbe; yankin Alagbaka; Ayede, Akure; Iloro Camp; da Ogbese a Karamar Hukumar ta Akure Arewa.

“Dangane da rikicin harbin shanu, muna da Umai Jibril da Hassan. Wannan ya kawo jimillar wadanda ake gabatarwa a nan kan wadannan laifuka zuwa 34, yayin da wadanda ba a gabatar da su ba, wadanda ake bincike a kansu a halin yanzu, suna 61.

“Ina so in rubuta a tarihi cewa mun sami nasarar cimma wannan sakamakon ne ta hanyar hadin gwiwar dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman ’yan sanda, NSCDC, DSS, da Rundunar Sojin Nijeriya,” in ji shi.

Adeleye ya gargadi masu laifi da su daina aikata laifuffukansu ko kuma su fuskanci mataki mai tsanani daga hukumomin tsaro.

“Jihar Ondo ba wurin tsira bane ga masu laifi. Za mu ci gaba da hadin gwiwa da hukumomi masu alaka domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi,” in ji Kwamandan Amotekun.

Ondo
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Ondo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.