ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Masu Garkuwa Ne 12 Da Wasu 83 A Jihar Ondo

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
Ondo

Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wadda aka fi sani da Amotekun Corps, ta kama akalla mutane 95 da ake zargin aikata laifuka a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

A cewar rundunar, kama wadannan mutane ya samu ne ta hanyar hadin gwiwa da jami’an ofishin rundunar ‘yan sanda na jihar, Nigeria Security and Civil Defence Corps, Department of State Services, da kuma sojojin Nijeriya.

  • Darussa Daga Ramadan Na (2)
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Kwamandan Amotekun na jihar, Akogun Adeleye, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Kwamandan ya ce wadanda aka kama ana zargin su da aikata laifuka kamar satar mutane (kidnapping), sata, fashi da makami, da kuma hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Ya bayyana wasu daga cikin wadanda ake zargin kamar haka: Bictor, mai shekara 31; Jonathan, mai shekara 34; Akpan, mai shekara 35; Aliu, mai shekara 27; Sanni, mai shekara 20; Adeoye, mai shekara 44; Ayodeji, mai shekara 50; Abdullahi, mai shekara 24; Doman, mai shekara 25; Isaac, mai shekara 20; Peter, mai shekara 25; da Dada, mai shekara 42.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Adeleye ya ce, “A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman Amotekun, ’yansanda, hukumar farin kaya, da DSS, sun yi kokari matuka wajen bibiyar wadanda ake zargi, kuma hakan ya haifar da sakamako mai kyau sosai.”

“Mutum 61 da aka samu a cikin motar tirela, ana zargin su ne, kuma muna ci gaba da tantance su domin sanin matakin da za a dauka bayan an gama tantance su.

“Muna da mutum 19 da suka karya dokar jihar. Muna da uku da suka shafi rikicin harbin shanu tsakanin manoma da makiyaya, sannan muna da 12 da suka shafi satar mutane.

“Labarin mai dadi shi ne cewa wasu daga cikin wadanda ake zargin satar mutane an kama su ne a Karamar Hukumar Akure ta Arewa mai rikici, kuma muna da yakinin cewa wannan zai kawo zaman lafiya a yankin, musamman da ake gudanar da hadin gwiwar ayyukan tsaro a halin yanzu.”

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin satar mutane a wurare kamar Ilu-Abo, Akure; Idogun-Ugbe; yankin Alagbaka; Ayede, Akure; Iloro Camp; da Ogbese a Karamar Hukumar ta Akure Arewa.

“Dangane da rikicin harbin shanu, muna da Umai Jibril da Hassan. Wannan ya kawo jimillar wadanda ake gabatarwa a nan kan wadannan laifuka zuwa 34, yayin da wadanda ba a gabatar da su ba, wadanda ake bincike a kansu a halin yanzu, suna 61.

“Ina so in rubuta a tarihi cewa mun sami nasarar cimma wannan sakamakon ne ta hanyar hadin gwiwar dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman ’yan sanda, NSCDC, DSS, da Rundunar Sojin Nijeriya,” in ji shi.

Adeleye ya gargadi masu laifi da su daina aikata laifuffukansu ko kuma su fuskanci mataki mai tsanani daga hukumomin tsaro.

“Jihar Ondo ba wurin tsira bane ga masu laifi. Za mu ci gaba da hadin gwiwa da hukumomi masu alaka domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi,” in ji Kwamandan Amotekun.

Ondo
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Ondo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

Wakilin Sin: Japan Ba Ta Cancanci Neman Kujerar Dindindin A Kwamitin Sulhun MDD Ba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.