Ɗaya daga cikin jagororin ƙoƙarin kafa jam’iyyar ADA, Umar Ardo, ya sake bayyana damuwa kan zargin rashin bin ƙa’ida wajen rijistar Jam’iyyar NDC, yana mai alƙawarin kai ƙarar lamarin kotu.
Jam’iyyar ADA na daga cikin kungiyoyi 171 da suka nemi rijista a wajen INEC domin zama jam’iyyun siyasa.Sai dai a watan Fabrairu 2026, INEC ta bayyana cewa kungiyoyi biyu ne kaɗai aka amince da su daga cikin waɗanda suka nema.
A wani taron tuntuba da shugabannin jam’iyyun siyasa a Abuja, shugaban INEC, Joash Amupitan, ya ce, jam’iyyar DLA ce kaɗai aka yi wa rijista daga cikin ƙungiyoyin, yayin da aka yi wa NDC rijista bisa umarnin kotu.
Sai dai yayin wata hira da ya yi a ‘Trust TV’, Ardo ya zargi INEC da kauce wa ƙa’idojinta ta hanyar yi wa wata jam’iyya rijista ba tare da ta bi cikakken tsarin tantancewa ba.
A nasa ɓangaren, jam’iyyar NDC ta bakin sakatarenta na ƙasa, Ikenna Enekweizu, ta bayyana zargin Ardo a matsayin marar tushe kuma mai ruɗarwa.
Rahotanni sun nuna cewa Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso sun shiga jam’iyyar NDC bayan ficewarsu daga ADC.
An kuma tabbatar da rajistar su a matsayin mambobin jam’iyyar a hedikwatar ta a Abuja, inda aka ba su katunan zama memba.
A wata hira da ya yi da DCL Hausa, Ardo ya dage cewa rijistar NDC na cike da kura-kurai, yana mai cewa zai kai ƙarar lamarin gaban kotu domin a warware matsalar.















Discussion about this post