Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce a shirye kasarsa take ta ci gaba da hada hannu da kasar Rasha karkashin tsare-tsaren Kwamitin Sulhu na MDD, da tuntubar juna kan manyan batutuwa a lokutan da suka dace da hada karfi da karfe wajen yayyafawa yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya ruwan sanyi, da kare zaman lafiya a yankin da daukaka tsaro a duniya.
Wang Yi wanda kuma mamba ne na ofishin siyasa na Kwamitin Kolin JKS, ya bayyana haka ne jiya Lahadi, yayin zantawa ta wayar tarho da ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov.
Da yake bayyana Sin a matsayin mai goyon bayan warware rikicin kasa da kasa da ma na yankuna ta hanyar tattaunawa da yarjeniyoyi, Wang Yi ya ce yanayin yankin Gabas ta Tsakiya na ci gaba da tabarbarewa, kuma har yanzu rikici na karuwa, yana mai cewa mafita ga tabbatar da zirga-zirga ta Mashigin Hormuz ta dogara ne kan dakatar da bude wuta da wuri da kawo karshen yakin.
A nasa bangare, Sergei Lavrov ya ce Rasha ta damu matuka da ci gaba da karuwar zaman dar-dar a yankin.
Game da rikicin da ke wakana da batun Mashigin Hormuz, ministan ya ce a ganin Rasha, dole ne a dakatar da ayyukan soji nan take, kuma a yi kokarin komawa ga warware batun a siyasance ta hanyar diflomasiyya domin maganin rikicin daga tushe, kana Kwamitin Sulhu na MDD ta taka muhimmiyar rawa kan hakan. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post