Kasar Sin ta tsara kaddamar da aikin binciken duniyar wata na Chang’e-7 a rabi na biyu na shekarar 2026.
Hukumar kula da harkokin sama jannati ta kasar Sin ce ta sanar da hakan a yau Juma’a, inda ta ce tuni aka kai na’urar da za ta gudanar da aikin binciken na Chang’e-7, cibiyar harba kumbuna ta Wenchang da ke lardin Hainan na kudancin kasar Sin, za kuma a gudanar da gwaje-gwajen share fagen aikin kamar yadda aka tsara.
Aikin binciken na Chang’e-7 na da nufin samar da nasarori a muhimman fannonin fasahohi a saman duniyar wata, kamar sauka cikin sauki dai-dai inda aka tsara da motsin na’urar da binciken ramukan dake duniyar.
Haka kuma, aikin zai kunshi hadin gwiwar kasa da kasa. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post