Shugaban gwamnatin Tarayyar Jamus Friedrich Merz yana gudanar da ziyarar aikinsa ta farko a hukumance a kasar Sin tsakanin ranekun 25 da 26 ga watan Fabrairu, 2026, bisa gayyatar takwaransa na Sin Li Qiang. Tawagar shugaban da ta kunshi wakilan bangaren tattalin arzikin Jamus 30 ta yi masa rakiya a ziyarar.
A lokacin ziyarar Merz a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da Merz, kuma firaministan kasar Li Qiang ya tattauna da shi. Shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan dangantakar Sin da Jamus, da batutuwan yanki da na kasa da kasa, da kuma batutuwan da suka shafi manufofin tattalin arziki.
Bangarorin biyu sun darajanta kyakkyawan hadin gwiwa a karkashin tsarin cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Jamus, kuma sun yarda cewa mutunta juna da cin moriya tare, da ci gaba da tattaunawa a bude, da kuma hadin gwiwa don fuskantar kalubalen gama-gari su ne muhimman ka’idojin bunkasa dangantakar Sin da Jamus. Wannan ziyara ta kawo sabon karfi ga bunkasar dangantakar abota ta hadin gwiwar kasashen biyu. Bangarorin biyu sun jaddada muhimmancin tsarin tattaunawa tsakanin gwamnatocin Sin da Jamus wajen ciyar da hadin gwiwar kasashen biyu gaba.
Kazalika, bangaren Jamus ya sake maimaita nacewa ga manufar kasar Sin daya tak a duniya.(Amina Xu)













Discussion about this post