Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a yau Alhamis cewa, ziyarar da shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya kawo kasar Sin tana da alfanu da kuma ma’ana, tana mai jaddada aniyar kasashen biyu wajen kiyaye zaman lafiya mai dorewa, da kara zurfafa hadin gwiwar moriyar juna, da magance sabanin ra’ayi ta hanyar tattaunawa ta gaskiya, da bude kofa da kuma girmama juna.
Mai magana da yawun ma’aikatar, Mao Ning ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai na yau da kullum, a yayin da take amsa wata tambaya mai nasaba da hakan.
Mao ta ce, shugabannin kasashen biyu sun yi imanin cewa, ya kamata Sin da Jamus su inganta tuntubar juna bisa manyan tsare-tsare, da zurfafa amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye hadin gwiwar bude kofa ga juna, da goyon bayan tsarin mabambantan bangarori da cinikayya cikin ‘yanci, da kare matsayin MDD, da bin tafarkin manufofi da ka’idojin kundin tsarin MDD, da ci gaba da zurfafa kawancensu a dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare.
Ta kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta dauki wannan ziyara a matsayin wata dama ta yin hadin gwiwa da bangaren Jamus don bude wani sabon babi na huldar dake tsakanin Sin da Jamus, da sanya kwanciyar hankali da karin kuzari mai kyau a duniya mai cike da sauyi da kuma tashin-tashina. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post