Gwamnatin Jihar Katsina ta amince da bayar da alawus na Naira 30,000 duk wata ga malaman da aka tura zuwa yankunan karkara, a wani yunƙuri na ƙara wa ma’aikatan ƙwarin gwiwa da kuma magance ƙarancin ma’aikata a yankunan karkara.
An yanke wannan shawarar ne a taron Majalisar Zartarwa ta Jiha karo na 18 da aka gudanar a ranar Laraba, wanda Gwamna Dikko Radda ya jagoranta.
- Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
- Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky
Da yake magana da manema labarai a ranar Alhamis, Kwamishinan Ilimi na karatun matakin farko da sakandare, Yusuf Suleiman-Jibia, ya bayyana cewa, alawus ɗin wanda aka tsara biya a kowane zangon karatu, an tsara shi ne don “ƙarawa malaman ƙwarin gwiwa” da kuma rage wa malaman nauyin kuɗin motar zuwa makarantun da aka tura su.
Suleiman-Jibia ya ƙara sanar da cewa, majalisar ta amince da kafa Cibiyoyin Horar da Malamai a Katsina, Daura, da Funtua.
“Cibiyoyin za su taimaka wajen haɓaka tsarin koyarwar malaman domin samar da ingantaccen ilimi ga ɗalibai a faɗin jihar,” in ji shi














