Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ya ce tun bayan fara aiwatar da manufar soke haraji kan kayayyakin kasashen Afrika masu huldar diplomasiyya da kasar Sin sama da kwanaki 20 da suka gabata, kashi-kashi na kayayyaki da dama daga nahiyar Afrika sun samu sahalewar kwastam a tashoshin ruwa daban-daban da ke fadin kasar Sin.
Guo Jiakun ya bayyana haka ne yau, lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da yanayin aiwatar da manufar kasar Sin ta soke haraji ga kasashen Afrika 53, wadda ta fara aiki a ranar 1 ga watan Mayu. Kakakin ya kara da cewa, manufar ba kara yawan kayayyakin Afrika a cikin kasuwar kasar Sin da rage kudin da ake kashewa na cinikayya kadai ta yi ba, har da karawa ’yan kasuwar nahiyar kwarin gwiwa.
Guo Jiakun ya ce kasar Sin za ta ci gaba da tattaunawa da rattaba hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwar tattalin arziki domin samun ci gaba na bai daya da kasashen Afrika masu ruwa da tsaki.
Yana mai cewa manufar ita ce kafa wani tsarin hadin gwiwar cinikayya da tattalin arziki mai dorewa da karko da tabbaci, wanda zai tabbatar da shirin soke harajin ya gudana yadda ya kamata tare da kare makomar ingantaccen hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Afrika. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post