Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana yadda wasu mutane suka yi ƙoƙarin tayar da rikici tsakaninsa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, jim kaɗan bayan fara mulkinsu.
Ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Yakubu Gowon, mai taken “My Life of Duty and Allegiance”.
Shettima ya ce wasu mutane da ya ce daga Jihar Borno suke sun je wajen Tinubu suna cewa yana shirin kashe shi domin ya karɓi mulki.
Ya ce: “Bayan watanni uku da rantsar da mu, wasu mutane suka je suka gaya wa Tinubu cewa ina shirin kashe shi in karɓi mulki. Shugaban Ƙasa ya kira ni ya ce ‘zauna! Mutanen ka sun zo suna cewa ka daina saka waɗancan rigunan Shettima.’”
Ya ƙara da cewa Tinubu ya bayyana masa cewa labarin bai gamsar ba, domin ba shi da tushe.
A cewarsa, “Sun ce bayan zaɓe ina shirin amfani da riguna domin in kashe shi in karɓi mulki. Amma daga baya Tinubu ya saka rigunan, domin ba ya yarda da camfi ko irin wannan tunani.”
Shettima ya shawarci ƴan Nijeriya da su kasance masu haɗin kai da kuma zama ƴan’uwan juna maimakon masu raba kawuna da juna.















Discussion about this post