ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Adadin Matan Nollywood Da Suka Musulunta?

by Sulaiman
4 years ago
Mercy

Mercy

Yau filin namu zai kawo muku shahararrun jaruman matan Nollywood da kaddarar Ubangiji ta ja su, suka sauya Addinin da suka dade aciki zuwa sabon addinin da suka sauya – Musulunci.

1.  Akindele Funke.

Nollywood
Funke

Fitacciyar jaruma, Funke Akindele, ta koma musulunci ne bayan ta auri Alhaji Kehinde Almaroof Oloyede, wanda aka daura aurensu a ranar 24 ga watan Mayu, 2012. Ta Musulunta ne bayan ta auri mijinta, Almaroof Oloyede wanda shima musulmi ne, Funke ta sauya sunanta zuwa Khadijat.

ADVERTISEMENT

2.  Liz Da Silva

Nollywood
lizz-da-silva

Sananniyar jaruma da aka fi sani da Liz and Silva, ta taso a addinin kiristanci, har sai da ta haifi danta na fari da wani musulmi da ba’a tantance waye ba, amma dai ana kiransa da suna Olaoye. Bayan ta haifi dan nasu ne, sai Lizzie din da danta suka canja addini suka koma musulunci, inda ta canja sunan ta zuwa Ai’shat.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

3. Lizzy Anjolin

Nollywood
lizzy-anjolin

Jarumar fim Elizabeth Anjorin, wadda kuma ake kira Lizzy Anjolin, itama Kirista ce a baya, amma daga baya sai ta koma musulunci domin radin kanta, saboda tace addinin yana burgeta. Ta canja sunan ta izuwa Sakinat da Aishat, inda ta canja sunan yar ta, kuma ya koma Rufaida.

4. Fathia Balogun

Nollywood
fathia

Fitacciyar Jaruma Fathia Balogun, ta tashi ne a gidan da suke bin, darikar cocin Roman Katolika. Bayan ta yi imani da wadansu mala’iku na kusa da Allah, kamar yadda darikar ke da imanin hakan, daga karshe kawai sai ta karbi addinin musulunci. Ta canja sunan ta zuwa Fatiha, kafin daga bisani ta auri wani darakta mai suna Said Balogun.

5. Mercy Aigbe

Nollywood
Mercy

Darakta Kazim Adeoti da Mercy Aigbe, sunyi auren su ne a kebance. Kazim musulmi ne, kyawawan halayyar addinin mijin nata da tsarin tufafin Matan musulmi ne ya birge Jarumar ta sauya addininta zuwa Musulunci. Mercy Aigbe ta sauya sunanta zuwa Minna.

6. Bimpe Mo
Uwargida ga jarumin fim din Nollywood mai suna Latif Dimeji, ta musulunta ne a karshen shekarar da ta wuce, bayan auren su da jarumin. Mo Bimpe ta Sauya sunanta zuwa Rahmatullah.

Daga Shafin Labarun Hausa

Nollywood
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Nollywood
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Nollywood
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Dan Ta’addar Da Aka Nada Sarauta A Zamfara Ya Kashe Mutum 100 A Katsina – ‘Yansanda

Dan Ta'addar Da Aka Nada Sarauta A Zamfara Ya Kashe Mutum 100 A Katsina - 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.