ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kogi Ta Rufe Kasuwanni Da Filayen Motoci Don Fitar Da ‘Yan Ta’adda

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi ta bayar da umarnin rufe wasu kasuwanni da filayen motoci na wucin gadi a sassa daban-daban na jihar, a matsayin wani bangare na tsauraran ayyukan tsaro da aka sanya domin fitar da ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da sauran masu aikata laifuka.

An sanar da wannan mataki ne a cikin wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Bayani da Sadarwa, Kingsley Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi, kuma aka bai wa PUNCH Metro.

Sanarwar ta bayyana cewa rufe kasuwanni da filayen motoci na wucin gadi ya shafi wasu kasuwanni da filayen motoci a yankin Kogi ta Yamma na Majalisar Dattawa da wuraren da ke makwabtaka da shi, yayin da hukumomin tsaro ke kara karfafa ayyukan tsabtace yankuna cikin hadin kai.

ADVERTISEMENT

Fanwo ya ce wannan mataki an tsara shi ne domin kawo cikas ga harkokin laifi ta hanyar takaita motsi da kuma katse hanyoyin samun abinci, kayan masarufi da sauran tallafi da ‘yan ta’adda da masu ba su bayanai ke amfani da su.

Ya kara da cewa, ayyukan na gudana ne tare da hadin gwiwar Ofishin Mashawarcin Tsaron Kasa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Rufewar ta wucin gadi an yi shi ne domin hana masu laifi damar motsi da samun hanyoyin tallafi yayin aikin tsaro,” in ji shi.

Wannan umarni ya shafi al’ummomi a cikin kananan hukumomi guda bakwai na jihar.

A Karamar Hukumar Lokoja, wuraren da abin ya shafa sun hada da Kasuwar Oshokoshoko da Filin Motoci, da kuma kasuwanni da filayen motoci a Jakura, Ogbagbon, Agbaja, Atsawa, Obajana, Apata, Abugi, Amomi, Ebee da Budon.

A Karamar Hukumar Kabba-Bunu, rufe kasuwanni da filayen motoci ya shafi wurare kamar Ike Bunu, Aba Marian (Isado), Ofere, Abaa Dola (Ihale Bunu), Aiyede, Oke Offin, Aiyegunle Bunu, Okebukun, Odo Ape Bunu, Agbadu Bunu da Agbede Apa Bunu.

A Karamar Hukumar Yagba West, al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Okoloke, Isanlu Esa, Okunran, Ogbe, Ejiba, Odo Eri, Igbaruku, Iyamerin, Ogga, Omi, Odo Ara da Oke Ere.

A Karamar Hukumar Yagba East, kasuwanni da filayen motoci a Irunda Ile, Iyeh Ilotin, Gada, Odogbe da Ilafin ma an rufe su na wucin gadi.

A Karamar Hukumar Kogi, umarnin ya shafi Kasuwar Shinkafa a Adingere, Koton Karfe, Okpareke da Girinya; Kasuwar Kubewa a Opanda; da Kasuwar Kayayyakin Da Ba Su Dorewa a Edeha.

Kasuwanni da filayen motoci a Otafun Amuro, Oroke Amuro, Takete Ide Amuro, Okeagi, Illai, Ilemo da Ijagbe a Karamar Hukumar Mopamuro shima abin ya shafa.

A Karamar Hukumar Ijumu, kasuwannin da za su kasance a rufe har tsawon lokacin ayyukan tsaro sun hada da: Ayegunle Gbedde, Iyah Gbedde, Ayetoro Gbedde, Ayeh Gbedde, Iluhagba, Odokoro da Okoro.

Kogi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Kogi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano

Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.