ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kogi Ta Rufe Kasuwanni Da Filayen Motoci Don Fitar Da ‘Yan Ta’adda

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
Kogi

Gwamnatin Jihar Kogi ta bayar da umarnin rufe wasu kasuwanni da filayen motoci na wucin gadi a sassa daban-daban na jihar, a matsayin wani bangare na tsauraran ayyukan tsaro da aka sanya domin fitar da ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da sauran masu aikata laifuka.

An sanar da wannan mataki ne a cikin wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Bayani da Sadarwa, Kingsley Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi, kuma aka bai wa PUNCH Metro.

Sanarwar ta bayyana cewa rufe kasuwanni da filayen motoci na wucin gadi ya shafi wasu kasuwanni da filayen motoci a yankin Kogi ta Yamma na Majalisar Dattawa da wuraren da ke makwabtaka da shi, yayin da hukumomin tsaro ke kara karfafa ayyukan tsabtace yankuna cikin hadin kai.

ADVERTISEMENT

Fanwo ya ce wannan mataki an tsara shi ne domin kawo cikas ga harkokin laifi ta hanyar takaita motsi da kuma katse hanyoyin samun abinci, kayan masarufi da sauran tallafi da ‘yan ta’adda da masu ba su bayanai ke amfani da su.

Ya kara da cewa, ayyukan na gudana ne tare da hadin gwiwar Ofishin Mashawarcin Tsaron Kasa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

“Rufewar ta wucin gadi an yi shi ne domin hana masu laifi damar motsi da samun hanyoyin tallafi yayin aikin tsaro,” in ji shi.

Wannan umarni ya shafi al’ummomi a cikin kananan hukumomi guda bakwai na jihar.

A Karamar Hukumar Lokoja, wuraren da abin ya shafa sun hada da Kasuwar Oshokoshoko da Filin Motoci, da kuma kasuwanni da filayen motoci a Jakura, Ogbagbon, Agbaja, Atsawa, Obajana, Apata, Abugi, Amomi, Ebee da Budon.

A Karamar Hukumar Kabba-Bunu, rufe kasuwanni da filayen motoci ya shafi wurare kamar Ike Bunu, Aba Marian (Isado), Ofere, Abaa Dola (Ihale Bunu), Aiyede, Oke Offin, Aiyegunle Bunu, Okebukun, Odo Ape Bunu, Agbadu Bunu da Agbede Apa Bunu.

A Karamar Hukumar Yagba West, al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Okoloke, Isanlu Esa, Okunran, Ogbe, Ejiba, Odo Eri, Igbaruku, Iyamerin, Ogga, Omi, Odo Ara da Oke Ere.

A Karamar Hukumar Yagba East, kasuwanni da filayen motoci a Irunda Ile, Iyeh Ilotin, Gada, Odogbe da Ilafin ma an rufe su na wucin gadi.

A Karamar Hukumar Kogi, umarnin ya shafi Kasuwar Shinkafa a Adingere, Koton Karfe, Okpareke da Girinya; Kasuwar Kubewa a Opanda; da Kasuwar Kayayyakin Da Ba Su Dorewa a Edeha.

Kasuwanni da filayen motoci a Otafun Amuro, Oroke Amuro, Takete Ide Amuro, Okeagi, Illai, Ilemo da Ijagbe a Karamar Hukumar Mopamuro shima abin ya shafa.

A Karamar Hukumar Ijumu, kasuwannin da za su kasance a rufe har tsawon lokacin ayyukan tsaro sun hada da: Ayegunle Gbedde, Iyah Gbedde, Ayetoro Gbedde, Ayeh Gbedde, Iluhagba, Odokoro da Okoro.

Kogi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kogi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano

Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.