Gobara ta sake tashi a kasuwar Singa da ke Jihar Kano, ƙasa da makonni biyu bayan wata gobara ta auku a kasuwar.
Shugaban ƙungiyar masu dakon kaya ta kasuwar, Hamisu Dan Hisbah, ya tabbatar da lamarin da yammacin ranar Asabar.
- Kogi Ta Rufe Kasuwanni Da Filayen Motoci Don Fitar Da ‘Yan Ta’adda
- Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam
Ya ce gobarar ta tashi ne kimanin mintuna 10 kafin ya yi magana da Leadership Hausa, kuma har yanzu ba a san musabbabin tashinta ba.
Ma’aikatan kashe gobara sun isa wurin suna ƙoƙarin daƙile yaɗuwar wutar.
Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a gano abin da ya haddasa gobarar ba, yayin da jami’an ke ci gaba da ƙoƙarin kashe wutar.
Makonni biyu da suka gabata, gobara ta tashi a Mazaf Plaza da ke cikin kasuwar, inda ta ƙone kayan miliyoyin Naira, lamarin da ya jefa ‘yan kasuwa cikin damuwa kan yawaitar gobara a kasuwar.















Discussion about this post