Yayin da ake buɗe makarantu a faɗin ƙasar nan, Ƙungiyar Iyaye da Malamai ta Nijeriya (PTA) ta roƙi gwamnatocin tarayya da jihohi da su tabbatar da tsaron ɗalibai da malamai. Shugaban PTA na ƙasa, Danjuma Haruna, wanda ya yi magana da jaridar LEADERSHIP jiya, ya bayyana cewa wajibi ne a ba tsaron ɗalibai da malamai muhimmanci a kowane lokaci.
Haruna ya jaddada cewa dole ne makarantu su kasance da isassun kayan aiki, kamar ajujuwa, ɗakunan gwaje-gwaje, wuraren koyon sana’o’i, da ɗakunan kwamfuta, domin samar da muhalli mai aminci da dacewa ga ɗalibai da ma’aikata.
- Jami’ar Kebbi Ta Karrama Gwamna Lawal da Digirin Girmamawa, Ta Yaba Da Ayyukan Raya Zamfara
- Komawar Abba APC: Maslahar Al’umma Ko Kasuwar Bukata?
Ya bayyana cewa PTA na aiki tare da hukumomin makarantu a matakai daban-daban daga makaranta, ƙaramar hukuma, jiha, har zuwa ƙasa baki ɗaya domin tabbatar da cewa dukkan makarantu sun shirya buɗewa, musamman ta fuskar tsaro da shirye-shiryen ilimi.
Yana tunatar da irin haɗarin da shan wuya da aka yi a baya ƙarƙashin shirin “Safe School”,
Haruna ya ce ƙungiyar ta yi aiki tare da jami’an tsaro, shugabannin al’umma da matasa wajen wayar da kan ɗalibai yadda za su kare kansu a lokacin gaggawa. Ya jaddada cewa waɗannan matakai na nufin kare rayuka ne, ba don tsoratarwa ba.
Shugaban PTA ya bayyana cewa ya gana da ministan tsaro domin ƙarfafa tsaro a makarantu na yini da na kwana, tare da sake jaddada shawarwarin mayar da makarantu masu rauni a ƙauyuka zuwa birane inda kulawar tsaro ta fi ƙarfi.
Haruna ya kuma roƙi Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya kasance mai saurin ɗaukar mataki wajen kare ɗalibai da malamai.
Haka kuma, ya shawarci gwamnonin jihohi da su yi amfani da kuɗaɗen tsaro cikin gaskiya tare da ba wa tsaron makarantu da al’ummominsu fifiko.















Discussion about this post