Babbar Kotun Jihar Kaduna ta ƙi amincewa da buƙatar ba ds belin tsohon gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufai.
Mai shari’a Dirisu Khobo ya yanke hukuncin ne a ranar Litinin, inda ya ce El-Rufai bai gabatar da hujjoji masu gamsarwa da za su sa kotun ta ba da belinsa ba.
El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhume tara da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta shigar a kansa, waɗanda suka haɗa da zargin amfani da muƙami ba bisa ƙa’ida ba da sauran laifuka.
Bai halarci kotun ba lokacin da aka yanke hukuncin.
Sai dai kotun ta umarci ICPC da ta bai wa El-Rufai damar ganin likitocinsa ko kuma zuwa duk wata cibiyar lafiya da ya zaɓa a Nijeriya idan yana buƙatar kulawar lafiya.
Kotun ta kuma umarci cewa El-Rufai ya ci gaba da zama a hannun ICPC, sannan ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranakun 7 da 8 ga watan Yuli domin ci gaba da shari’ar.
An fara gurfanar da El-Rufai a gaban kotu a watan Maris na shekarar 2026 tare da Amadu Sule, Manajan Daraktan kamfanin TMDK Terminal Limited.
Daga baya an gyara tuhume-tuhumen tare da cire Amadu Sule daga cikin shari’ar, wanda ya sa El-Rufai ya rage shi kaɗai da ke fuskantar tuhume-tuhume tara.














