Gwamnatin Tarayya ta samu nasarar gurfanar da wasu mutane biyar tare da ɗaure su bayan kotu ta same su da laifin kai makamai da alburusai ga ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram. Hukuncin ya fito ne daga Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarƙashin Mai Shari’a Binta Nyako.
Waɗanda aka yanke wa hukunci sun haɗa da Yusuf Muhammad (Bature), da Goni Ibrahim Bindi (Goni Mutuwa), da Sani Tukur (Danladi), da Mubarak Ibrahim da Musa Alhaji Adamu (Gado Banufe). An same su da laifukan haɗa baki wajen taimaka wa ‘yan ta’adda, da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma ɓoye bayanan da za su taimaka wajen cafke wani ɗan Boko Haram.
Bincike ya nuna cewa mutanen sun taimaka wajen jigilar bindigogi AK-103 guda 15 da harsasai 1,434 daga yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar zuwa wani da ake zargin ɗan Boko Haram ne mai suna Malam Ahmad a karamar hukumar Borgu ta Jihar Niger. An boye makaman ne a cikin buhunan busasshen kifi a wata mota mai lambar Nijar.
Kotun ta yanke wa kowannensu hukuncin zaman gidan yari na shekaru 25 a wasu tuhume-tuhume, shekaru 7 a wani laifi da kuma shekaru 20 a wani, amma ta umarci duk hukuncin ya tafi tare (concurrently). Kotun ta kuma ba da umarnin kwace dukkan makamai da alburusan da aka kama.














Discussion about this post