Ɗan takarar kujerar majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Sandamu, Daura da Mai’adua, kuma tsohon ɗan shugaban ƙasa, Yusuf Buhari, ya halarci zaɓen fidda gwani da aka gudanar a mazaɓar Kangiwa da ke Daura.
Da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala tantance al’ummar da suka hau layi domin cika sharuddan da jam’iyyar APC ta gindaya wajen gudanar da zaɓen fidda gwani, Hon. Yusuf Buhari ya bayyana gamsuwarsa kan yadda al’umma suka fito domin gudanar da zaɓen cikin lumana da tsari.
Ya ce fitowar jama’a da yadda suka nuna sha’awa wajen gudanar da zaɓen fidda gwani na ‘yan takarar majalisar dattawa a shiyyar Daura abin yabawa ne.
A zaɓen, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Nasiru Yahaya Daura, na fafatawa ne tare da Alhaji Ahmad Kabir, wanda aka fi sani da AK Canji.
Haka kuma, Yusuf Buhari ya bayyana fatan cewa al’umma za su ci gaba da bai wa jam’iyyar APC goyon baya a duk zaɓuɓɓukan da ke tafe.















Discussion about this post