A ranar Alhamis ne wata babbar kotun jihar Kano ta yanke wa wani Abdulaziz Adamu hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa laifin sacewa da kashe mai gidansa, Alhaji Ali Alhassan, bayan ya karɓi kuɗin fansa har Naira miliyan 15 daga iyalan wanda aka kashe.
An samu Adamu, mazaunin karamar hukumar Dawakin Kudu ta jihar Kano, da laifi kan tuhume-tuhume uku da suka shafi yaudara, garkuwa da mutane da kuma kisan kai.
- Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu Ƙara
- Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano
Lauyan masu gabatar da kara, Lamido Abba-Sorondinki, ya shaida wa kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin a ranar 16 ga Yuni, 2024, lokacin da ya hada baki da wani wanda ake kara na biyu don sace wanda aka kashe a Dawakin Kudu.
Ya ce, wanda ake kara ya nema kuma an bashi kudin fansa har Naira miliyan 15 daga iyalan wanda aka kashe kafin su kashe shi.
“Sun bugi wanda aka kashe a kai da ƙirji da sanda sannan daga baya suka binne gawar a gidan Adamu da ke Dawakin Kudu,” in ji mai gabatar da kara ga kotun.
Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Aisha Mahmoud ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da hujjoji game da karar da suka shigar a kan Adamu ba tare da wata shakka ba.
“Ina yanke wa Adamu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda ya buga wa wanda aka kashe sanda a kansa da ƙirjinsa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. Ubangiji ya yi masa rahama,” in ji ta.














