ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
6 months ago
Rake

Manoma da dama a Jihar Kano, sun bayyana fargabarsu, kan barkewar annobar wata cuta da ta yi sanadiyyar lalata Raken da suka shuka a gonakinsu.

Wannan annoba, ta bulla ne a kananan hukumomi uku da ake noman Raken a fadin jihar, wadda kuma ta lalata hektoci da dama da hakan zai iya haifar da karancinsa a bana.

  • Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed
  • Dabarun Sojoji Na Yaki Da Ta’addanci Ba Ya Aiki – Gwamnan Kebbi

Wasu daga cikin manoman Raken da abin ya shafa, sun bayyana cewa; sun gano bullar cutar ne a daidai lokacin da suka fara shirye-shiyen girbin Raken. A cewarsu, asarar da annobar ta jawo, ta kai ta akalla Naira biliyan biyu, inda kuma suka sanar da cewa; zai yi musu wuya, su sake yin wani noman a kakar noma ta badi, matukar mahukunta ba su dauki matakan gaggawa kan lamarin ba. Sun bayyana cewa, cutar ta yi wa daukacin gonakin da aka shuka Raken matukar illa, musamman a yankunan Dan Hassan, Garin Kaya, Tofa da kuma Gamadan.

ADVERTISEMENT

A cewar daya daga cikin manoman Raken a garin Kura, Malam Kawu Hayi, “Ba mu tsammaci cutar ta lalata gonakin Raken kamar haka ba, inda ya ce; lamarin ya fi yin kamari a garin Gamadan, wanda nan ne babban yankin da aka fi yin nomansa da kuma hada-hadar kasuwancinsa.Akasari dai, noman Raken shi ne kusan sana’ar da al’ummar yankin suka fi mayar da hankali a kai, wajen samun kudaden shiga, inda bullar cutar a yanzu za ta iya jawo samun marasa aikin yi”.

Rahotanni sun bayyana cewa, Raken da ba a riga an girbe shi ba, ya yi bakikkirin wasu kuma sun bushe. Shi ma wani nanomin Raken da ke yankin, Malam Isah Shu’aibu ya bayyana cewa; yankin ne kan gaba wajen noman Rake a daukacin fadin Arewacin kasar.”Muna kan shirye-shiryen girbe Raken, cutar ta bulla, wadda kuma ta lalata akasarin gonakin manoman Raken baki-daya, kazalika mun zuba dimbin kudade a aikin gonakin tare da bata lokacinmu, wajen yin aiki a gonakin namu, amma yanzu, komai ya lalace,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Har ila yau, ya yi gargadi da cewa; idan har ba a yi gaggawar dakile yaduwar cutar ba, hakan zai iya sanya wa manoma da dama a yankunan yin watsi da noman Rake a shekara mai zuwa, inda kuma wasunsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; illar cutar ta fara haifar da hauhawar farashinsa da kuma karancinsa. Wani babban dilan Raken, Danbaba Yunusa Dan Hassan, ya sanar da cewa; nan ba da jimawa ba, Raken zai yi karanci a wasu kasuwannin, matukar ba a dauki matakan gaggawa kan dakile yaduwar cutar ba, domin lamarin ya fi karfin manomansa, wajen lalubo mafita a kan matsalar.

Kazalika, manoman sun bayyana cewa; akwai bukatar mahukunta a bangaren aikin noma, su tura malaman gona domin duba irin illar da cutar ta yi a gonakin tare kuma da bayar da shawara kan lamarin.

Wani malamin gona a garin Kura Salisu Sa’ad, ya tabbatar da bullar cutar wanda ya ce; tuni ya tura zuwa gonakin da iftila’in ya afku, domin tantance irin barnar da cutar ta yi don daukar matakan da suka dace.Wata mai gudanar da bincike a Hukumar Aikin Noma (IITA), Dakta Wajiha Abdullahi Mu’az, ta danganta annobar a matsayin wata babbar barazana da ke bukatar daukar matakan gaggawa, domin dakile yaduwarta.

Rake
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Rake
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.