ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
7 months ago
Rake

Manoma da dama a Jihar Kano, sun bayyana fargabarsu, kan barkewar annobar wata cuta da ta yi sanadiyyar lalata Raken da suka shuka a gonakinsu.

Wannan annoba, ta bulla ne a kananan hukumomi uku da ake noman Raken a fadin jihar, wadda kuma ta lalata hektoci da dama da hakan zai iya haifar da karancinsa a bana.

  • Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed
  • Dabarun Sojoji Na Yaki Da Ta’addanci Ba Ya Aiki – Gwamnan Kebbi

Wasu daga cikin manoman Raken da abin ya shafa, sun bayyana cewa; sun gano bullar cutar ne a daidai lokacin da suka fara shirye-shiyen girbin Raken. A cewarsu, asarar da annobar ta jawo, ta kai ta akalla Naira biliyan biyu, inda kuma suka sanar da cewa; zai yi musu wuya, su sake yin wani noman a kakar noma ta badi, matukar mahukunta ba su dauki matakan gaggawa kan lamarin ba. Sun bayyana cewa, cutar ta yi wa daukacin gonakin da aka shuka Raken matukar illa, musamman a yankunan Dan Hassan, Garin Kaya, Tofa da kuma Gamadan.

ADVERTISEMENT

A cewar daya daga cikin manoman Raken a garin Kura, Malam Kawu Hayi, “Ba mu tsammaci cutar ta lalata gonakin Raken kamar haka ba, inda ya ce; lamarin ya fi yin kamari a garin Gamadan, wanda nan ne babban yankin da aka fi yin nomansa da kuma hada-hadar kasuwancinsa.Akasari dai, noman Raken shi ne kusan sana’ar da al’ummar yankin suka fi mayar da hankali a kai, wajen samun kudaden shiga, inda bullar cutar a yanzu za ta iya jawo samun marasa aikin yi”.

Rahotanni sun bayyana cewa, Raken da ba a riga an girbe shi ba, ya yi bakikkirin wasu kuma sun bushe. Shi ma wani nanomin Raken da ke yankin, Malam Isah Shu’aibu ya bayyana cewa; yankin ne kan gaba wajen noman Rake a daukacin fadin Arewacin kasar.”Muna kan shirye-shiryen girbe Raken, cutar ta bulla, wadda kuma ta lalata akasarin gonakin manoman Raken baki-daya, kazalika mun zuba dimbin kudade a aikin gonakin tare da bata lokacinmu, wajen yin aiki a gonakin namu, amma yanzu, komai ya lalace,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Har ila yau, ya yi gargadi da cewa; idan har ba a yi gaggawar dakile yaduwar cutar ba, hakan zai iya sanya wa manoma da dama a yankunan yin watsi da noman Rake a shekara mai zuwa, inda kuma wasunsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; illar cutar ta fara haifar da hauhawar farashinsa da kuma karancinsa. Wani babban dilan Raken, Danbaba Yunusa Dan Hassan, ya sanar da cewa; nan ba da jimawa ba, Raken zai yi karanci a wasu kasuwannin, matukar ba a dauki matakan gaggawa kan dakile yaduwar cutar ba, domin lamarin ya fi karfin manomansa, wajen lalubo mafita a kan matsalar.

Kazalika, manoman sun bayyana cewa; akwai bukatar mahukunta a bangaren aikin noma, su tura malaman gona domin duba irin illar da cutar ta yi a gonakin tare kuma da bayar da shawara kan lamarin.

Wani malamin gona a garin Kura Salisu Sa’ad, ya tabbatar da bullar cutar wanda ya ce; tuni ya tura zuwa gonakin da iftila’in ya afku, domin tantance irin barnar da cutar ta yi don daukar matakan da suka dace.Wata mai gudanar da bincike a Hukumar Aikin Noma (IITA), Dakta Wajiha Abdullahi Mu’az, ta danganta annobar a matsayin wata babbar barazana da ke bukatar daukar matakan gaggawa, domin dakile yaduwarta.

Rake
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
Rake
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.