ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
9 months ago
Rake

Manoma da dama a Jihar Kano, sun bayyana fargabarsu, kan barkewar annobar wata cuta da ta yi sanadiyyar lalata Raken da suka shuka a gonakinsu.

Wannan annoba, ta bulla ne a kananan hukumomi uku da ake noman Raken a fadin jihar, wadda kuma ta lalata hektoci da dama da hakan zai iya haifar da karancinsa a bana.

  • Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed
  • Dabarun Sojoji Na Yaki Da Ta’addanci Ba Ya Aiki – Gwamnan Kebbi

Wasu daga cikin manoman Raken da abin ya shafa, sun bayyana cewa; sun gano bullar cutar ne a daidai lokacin da suka fara shirye-shiyen girbin Raken. A cewarsu, asarar da annobar ta jawo, ta kai ta akalla Naira biliyan biyu, inda kuma suka sanar da cewa; zai yi musu wuya, su sake yin wani noman a kakar noma ta badi, matukar mahukunta ba su dauki matakan gaggawa kan lamarin ba. Sun bayyana cewa, cutar ta yi wa daukacin gonakin da aka shuka Raken matukar illa, musamman a yankunan Dan Hassan, Garin Kaya, Tofa da kuma Gamadan.

ADVERTISEMENT

A cewar daya daga cikin manoman Raken a garin Kura, Malam Kawu Hayi, “Ba mu tsammaci cutar ta lalata gonakin Raken kamar haka ba, inda ya ce; lamarin ya fi yin kamari a garin Gamadan, wanda nan ne babban yankin da aka fi yin nomansa da kuma hada-hadar kasuwancinsa.Akasari dai, noman Raken shi ne kusan sana’ar da al’ummar yankin suka fi mayar da hankali a kai, wajen samun kudaden shiga, inda bullar cutar a yanzu za ta iya jawo samun marasa aikin yi”.

Rahotanni sun bayyana cewa, Raken da ba a riga an girbe shi ba, ya yi bakikkirin wasu kuma sun bushe. Shi ma wani nanomin Raken da ke yankin, Malam Isah Shu’aibu ya bayyana cewa; yankin ne kan gaba wajen noman Rake a daukacin fadin Arewacin kasar.”Muna kan shirye-shiryen girbe Raken, cutar ta bulla, wadda kuma ta lalata akasarin gonakin manoman Raken baki-daya, kazalika mun zuba dimbin kudade a aikin gonakin tare da bata lokacinmu, wajen yin aiki a gonakin namu, amma yanzu, komai ya lalace,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau, ya yi gargadi da cewa; idan har ba a yi gaggawar dakile yaduwar cutar ba, hakan zai iya sanya wa manoma da dama a yankunan yin watsi da noman Rake a shekara mai zuwa, inda kuma wasunsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; illar cutar ta fara haifar da hauhawar farashinsa da kuma karancinsa. Wani babban dilan Raken, Danbaba Yunusa Dan Hassan, ya sanar da cewa; nan ba da jimawa ba, Raken zai yi karanci a wasu kasuwannin, matukar ba a dauki matakan gaggawa kan dakile yaduwar cutar ba, domin lamarin ya fi karfin manomansa, wajen lalubo mafita a kan matsalar.

Kazalika, manoman sun bayyana cewa; akwai bukatar mahukunta a bangaren aikin noma, su tura malaman gona domin duba irin illar da cutar ta yi a gonakin tare kuma da bayar da shawara kan lamarin.

Wani malamin gona a garin Kura Salisu Sa’ad, ya tabbatar da bullar cutar wanda ya ce; tuni ya tura zuwa gonakin da iftila’in ya afku, domin tantance irin barnar da cutar ta yi don daukar matakan da suka dace.Wata mai gudanar da bincike a Hukumar Aikin Noma (IITA), Dakta Wajiha Abdullahi Mu’az, ta danganta annobar a matsayin wata babbar barazana da ke bukatar daukar matakan gaggawa, domin dakile yaduwarta.

Rake
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Rake
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.