ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
7 months ago
Rake

Manoma da dama a Jihar Kano, sun bayyana fargabarsu, kan barkewar annobar wata cuta da ta yi sanadiyyar lalata Raken da suka shuka a gonakinsu.

Wannan annoba, ta bulla ne a kananan hukumomi uku da ake noman Raken a fadin jihar, wadda kuma ta lalata hektoci da dama da hakan zai iya haifar da karancinsa a bana.

  • Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed
  • Dabarun Sojoji Na Yaki Da Ta’addanci Ba Ya Aiki – Gwamnan Kebbi

Wasu daga cikin manoman Raken da abin ya shafa, sun bayyana cewa; sun gano bullar cutar ne a daidai lokacin da suka fara shirye-shiyen girbin Raken. A cewarsu, asarar da annobar ta jawo, ta kai ta akalla Naira biliyan biyu, inda kuma suka sanar da cewa; zai yi musu wuya, su sake yin wani noman a kakar noma ta badi, matukar mahukunta ba su dauki matakan gaggawa kan lamarin ba. Sun bayyana cewa, cutar ta yi wa daukacin gonakin da aka shuka Raken matukar illa, musamman a yankunan Dan Hassan, Garin Kaya, Tofa da kuma Gamadan.

ADVERTISEMENT

A cewar daya daga cikin manoman Raken a garin Kura, Malam Kawu Hayi, “Ba mu tsammaci cutar ta lalata gonakin Raken kamar haka ba, inda ya ce; lamarin ya fi yin kamari a garin Gamadan, wanda nan ne babban yankin da aka fi yin nomansa da kuma hada-hadar kasuwancinsa.Akasari dai, noman Raken shi ne kusan sana’ar da al’ummar yankin suka fi mayar da hankali a kai, wajen samun kudaden shiga, inda bullar cutar a yanzu za ta iya jawo samun marasa aikin yi”.

Rahotanni sun bayyana cewa, Raken da ba a riga an girbe shi ba, ya yi bakikkirin wasu kuma sun bushe. Shi ma wani nanomin Raken da ke yankin, Malam Isah Shu’aibu ya bayyana cewa; yankin ne kan gaba wajen noman Rake a daukacin fadin Arewacin kasar.”Muna kan shirye-shiryen girbe Raken, cutar ta bulla, wadda kuma ta lalata akasarin gonakin manoman Raken baki-daya, kazalika mun zuba dimbin kudade a aikin gonakin tare da bata lokacinmu, wajen yin aiki a gonakin namu, amma yanzu, komai ya lalace,” a cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Har ila yau, ya yi gargadi da cewa; idan har ba a yi gaggawar dakile yaduwar cutar ba, hakan zai iya sanya wa manoma da dama a yankunan yin watsi da noman Rake a shekara mai zuwa, inda kuma wasunsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; illar cutar ta fara haifar da hauhawar farashinsa da kuma karancinsa. Wani babban dilan Raken, Danbaba Yunusa Dan Hassan, ya sanar da cewa; nan ba da jimawa ba, Raken zai yi karanci a wasu kasuwannin, matukar ba a dauki matakan gaggawa kan dakile yaduwar cutar ba, domin lamarin ya fi karfin manomansa, wajen lalubo mafita a kan matsalar.

Kazalika, manoman sun bayyana cewa; akwai bukatar mahukunta a bangaren aikin noma, su tura malaman gona domin duba irin illar da cutar ta yi a gonakin tare kuma da bayar da shawara kan lamarin.

Wani malamin gona a garin Kura Salisu Sa’ad, ya tabbatar da bullar cutar wanda ya ce; tuni ya tura zuwa gonakin da iftila’in ya afku, domin tantance irin barnar da cutar ta yi don daukar matakan da suka dace.Wata mai gudanar da bincike a Hukumar Aikin Noma (IITA), Dakta Wajiha Abdullahi Mu’az, ta danganta annobar a matsayin wata babbar barazana da ke bukatar daukar matakan gaggawa, domin dakile yaduwarta.

Rake
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 
Rake
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

Hukumar Siyasa Ta Kwamitin Kolin JKS Ta Kira Taro Don Bitar Rahoton Binciken Yankuna

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.