Ana sa ran wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta ci gaba da sauraron ƙarar da ke ƙalubalantar ko tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan yana da damar tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Lauya Johnmary Jideobi ne ya shigar da ƙarar, inda yake neman kotu ta hana Jonathan sake tsayawa takara.
Lauyan ya buƙaci kotun ta fassara kundin tsarin mulki dangane da wa’adin mulkin shugaban ƙasa.
Ƙarar na tambayar ko Jonathan zai iya sake takara bayan ya kammala wa’adin marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua sannan daga baya ya yi cikakken wa’adi a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.
An dai taɓa sauraron shari’ar a baya amma aka ɗage ta saboda rashin halartar wasu ɓangarori.
Lamarin ya jawo muhawara a fannin siyasa da shari’a yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen zaɓen 2027.
Jonathan, wanda ya yi mulkin Nijeriya daga 2010 zuwa 2015, bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takara a 2027 ba.















Discussion about this post