Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin tarayya da ci gaba da ciwo basussuka fiye da kima duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga daga hauhawar farashin man fetur a kasuwannin duniya.
Atiku ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ci bashin cikin gida har Naira tiriliyan 24.7 tsakanin Janairu da Agusta 2026.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce adadin bashin ya ƙaru da kashi 90.5 cikin 100 idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 12.98 da aka ci bashi a makamancin lokacin shekarar 2025. Ya ce abin ya fi tayar da hankali ne saboda farashin ɗanyen mai ya tashi sama da farashin da aka yi amfani da shi wajen tsara kasafin kudin 2026.
Atiku ya ce cire tallafin man fetur da shawarar sauya tsarin musayar kuɗin Naira ya kamata su taimaka wajen rage matsin lamba kan kuɗaɗen gwamnati, maimakon ƙara dogaro da bashi. Ya kuma ce ƙaruwar bashin gwamnati na iya rage damar da kamfanoni masu zaman kansu ke samu wajen samun rance mai sauƙi.
A cewarsa, bashin da gwamnati ke karɓa yana ƙaruwa da sauri fiye da rancen da ake bai wa kamfanoni masu zaman kansu. Ya bayyana cewa rancen da aka bai wa gwamnati ya ƙaru da kashi 43 cikin 100, yayin da na kamfanoni masu zaman kansu ya ƙaru da kashi 9.6 cikin 100, lamarin da ya ce na iya ƙara tsadar samun jari ga ƴan kasuwa.
Atiku ya tambayi inda ƙarin kuɗaɗen shiga da gwamnati ke samu suke tafiya, yana mai cewa bai kamata a ci gaba da karɓar ɗimbin bashi a lokacin da ake samun ƙarin kuɗaɗen shiga ba.
Ya bayyana yadda ake tafiyar da tattalin arziƙin gwamnatin Tinubu a matsayin rashin bin ƙa’idojin kula da kasafin kuɗi, tare da yin kira da a samar da cikakken bayani kan yadda ake amfani da kuɗaɗen gwamnati.














