Yayin da duniya take sam-barka da amincewa da tsagaita wuta a tsakanin Iran da Amurka da wasu kawayenta, wani al’amari na son zuciya ya kunno kai yayin da ake kada kuri’ar neman amincewa da wani daftarin kuduri na amfani da karfin soji wajen rakiyar jiragen ruwa na kasuwanci a mashigin Hormuz, kwana daya kafin sanar da tsagaita wutar.
Kasashe 11 sun amince da daftarin kudurin, yayin da kasar Sin da Rasha suka hau kujerar na ki, kana kasashen Colombia da Pakistan suka dauki matsayin ’yan ba ruwanmu. Wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya ya kafa hujjar kasarsa ta hawa kujerar na ki da cewa, kudurin ya gaza fito da asalin musabbabin rikicin baro-baro, wanda matukar ana son magancewa, wajibi ne a faro daga tushe, kuma a yi adalci ga kowane bangare.
Wannan matsayi da kasar Sin ta dauka, tunatarwa ce ga kasashen duniya game da sashe na 2, karamin sashe na 4 da kuma sashe na 51 na kundin Majalisar Dinkin Duniya da ya haramta amfani da karfi a kan wata kasa, tare da jaddada wajibcin bin hanyoyin sulhu wajen warware takaddama.
Ba ma wai kawai matakin da Amurka da Isra’ila suka dauka na kaddamar da hare-hare a kan Iran haramtacce ne da ya yi karan-tsaye ga kundin Majalisar Dinkin Duniya ba, an dauke shi ne ana kan tattaunawar zaman lafiya. Bugu da kari, idan aka dubi hujjar nukiliya da aka bayar ta kai hare-haren, ita kanta Isra’ila da ta zama kanwa uwar-gamin abun, ba ta cikin kasashen da suka rattaba hannu kan haramcin makaman nukiliya a duniya. Kuma a tambayi hukumar IAEA mai kula da makamashin nukiliya ta duniya, shin ko a mafarki ta taba kai ziyara Isra’ila da nufin binciken sha’anin nukiliyar kasar?
Matukar ana son magance matsala da gaske, daga tushe ake tumbuke jijiyar musabbabinta, kuma wannan shi ne adalcin da kasar Sin ta nemi a yi wa kowane bangare na rikicin, domin idan ba a faro daga nan ba, zai zamo an kashe maciji ne amma ba a sare kansa ba.
A lokacin da Isra’ila take farko-farkon kaddamar da hare-harenta a zirin Gaza wadanda suka salwantar da dubban rayukan fararen hula, a wani tsokaci da ya yi, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce, ya kamata a duba matsalar daga tushe, ma’ana, mene ne ya haddasa harin da Hamas ta kai ranar 7 ga Oktobar 2023, domin kamar yadda ya ce, komin raunin mutum idan tura ta kai shi bango, zuciyarsa tana kekashewa. Amma me ya biyo bayan maganar tasa? Yekuwar a tumbuke shi daga kujerarsa ta MDD daga bangaren Isra’ila da wasu kawayenta, maimakon duba abin da idon basira.
A wata mukalar da ya taba rubutawa, masanin zamantakewar dan’adam, farfesan farfesoshi kan sulhunta rikicin kasa da kasa a Jami’ar Notre Dames, John Paul Lederach ya bayyana cewa, zaman lafiya mai dorewa yana samuwa ne daga magance rikici daga tushe. Shi ma masanin zamantakewa Johan Galtun a wata mukalarsa ya bayyana cewa, rikici yana kunno kai ne daga rashin adalci da daidaito.
A halin yanzu dai, kasar Sin ta haska hanya game da komawa turbar adalci a fagen kasa da kasa, kuma tambayar da mutane da dama ke yi ita ce, sai yaushe wasu kasashe za su warke daga makantarsu ta fadar gaskiya da adalci? (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post