ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuri’ar Kwamitin Sulhu: Sai Yaushe Wasu Kasashen Duniya Za Su Warke Makantarsu?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sulhu

Yayin da duniya take sam-barka da amincewa da tsagaita wuta a tsakanin Iran da Amurka da wasu kawayenta, wani al’amari na son zuciya ya kunno kai yayin da ake kada kuri’ar neman amincewa da wani daftarin kuduri na amfani da karfin soji wajen rakiyar jiragen ruwa na kasuwanci a mashigin Hormuz, kwana daya kafin sanar da tsagaita wutar.

Kasashe 11 sun amince da daftarin kudurin, yayin da kasar Sin da Rasha suka hau kujerar na ki, kana kasashen Colombia da Pakistan suka dauki matsayin ’yan ba ruwanmu. Wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya ya kafa hujjar kasarsa ta hawa kujerar na ki da cewa, kudurin ya gaza fito da asalin musabbabin rikicin baro-baro, wanda matukar ana son magancewa, wajibi ne a faro daga tushe, kuma a yi adalci ga kowane bangare.

Wannan matsayi da kasar Sin ta dauka, tunatarwa ce ga kasashen duniya game da sashe na 2, karamin sashe na 4 da kuma sashe na 51 na kundin Majalisar Dinkin Duniya da ya haramta amfani da karfi a kan wata kasa, tare da jaddada wajibcin bin hanyoyin sulhu wajen warware takaddama.

ADVERTISEMENT

Ba ma wai kawai matakin da Amurka da Isra’ila suka dauka na kaddamar da hare-hare a kan Iran haramtacce ne da ya yi karan-tsaye ga kundin Majalisar Dinkin Duniya ba, an dauke shi ne ana kan tattaunawar zaman lafiya. Bugu da kari, idan aka dubi hujjar nukiliya da aka bayar ta kai hare-haren, ita kanta Isra’ila da ta zama kanwa uwar-gamin abun, ba ta cikin kasashen da suka rattaba hannu kan haramcin makaman nukiliya a duniya. Kuma a tambayi hukumar IAEA mai kula da makamashin nukiliya ta duniya, shin ko a mafarki ta taba kai ziyara Isra’ila da nufin binciken sha’anin nukiliyar kasar?

Matukar ana son magance matsala da gaske, daga tushe ake tumbuke jijiyar musabbabinta, kuma wannan shi ne adalcin da kasar Sin ta nemi a yi wa kowane bangare na rikicin, domin idan ba a faro daga nan ba, zai zamo an kashe maciji ne amma ba a sare kansa ba.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A lokacin da Isra’ila take farko-farkon kaddamar da hare-harenta a zirin Gaza wadanda suka salwantar da dubban rayukan fararen hula, a wani tsokaci da ya yi, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce, ya kamata a duba matsalar daga tushe, ma’ana, mene ne ya haddasa harin da Hamas ta kai ranar 7 ga Oktobar 2023, domin kamar yadda ya ce, komin raunin mutum idan tura ta kai shi bango, zuciyarsa tana kekashewa. Amma me ya biyo bayan maganar tasa? Yekuwar a tumbuke shi daga kujerarsa ta MDD daga bangaren Isra’ila da wasu kawayenta, maimakon duba abin da idon basira.

A wata mukalar da ya taba rubutawa, masanin zamantakewar dan’adam, farfesan farfesoshi kan sulhunta rikicin kasa da kasa a Jami’ar Notre Dames, John Paul Lederach ya bayyana cewa, zaman lafiya mai dorewa yana samuwa ne daga magance rikici daga tushe. Shi ma masanin zamantakewa Johan Galtun a wata mukalarsa ya bayyana cewa, rikici yana kunno kai ne daga rashin adalci da daidaito.

A halin yanzu dai, kasar Sin ta haska hanya game da komawa turbar adalci a fagen kasa da kasa, kuma tambayar da mutane da dama ke yi ita ce, sai yaushe wasu kasashe za su warke daga makantarsu ta fadar gaskiya da adalci? (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sulhu
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sulhu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Maraba Da Shirin Tsagaita Wuta A Rikicin Iran

Kasar Sin Na Maraba Da Shirin Tsagaita Wuta A Rikicin Iran

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.