ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuri’ar Kwamitin Sulhu: Sai Yaushe Wasu Kasashen Duniya Za Su Warke Makantarsu?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sulhu

Yayin da duniya take sam-barka da amincewa da tsagaita wuta a tsakanin Iran da Amurka da wasu kawayenta, wani al’amari na son zuciya ya kunno kai yayin da ake kada kuri’ar neman amincewa da wani daftarin kuduri na amfani da karfin soji wajen rakiyar jiragen ruwa na kasuwanci a mashigin Hormuz, kwana daya kafin sanar da tsagaita wutar.

Kasashe 11 sun amince da daftarin kudurin, yayin da kasar Sin da Rasha suka hau kujerar na ki, kana kasashen Colombia da Pakistan suka dauki matsayin ’yan ba ruwanmu. Wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya ya kafa hujjar kasarsa ta hawa kujerar na ki da cewa, kudurin ya gaza fito da asalin musabbabin rikicin baro-baro, wanda matukar ana son magancewa, wajibi ne a faro daga tushe, kuma a yi adalci ga kowane bangare.

Wannan matsayi da kasar Sin ta dauka, tunatarwa ce ga kasashen duniya game da sashe na 2, karamin sashe na 4 da kuma sashe na 51 na kundin Majalisar Dinkin Duniya da ya haramta amfani da karfi a kan wata kasa, tare da jaddada wajibcin bin hanyoyin sulhu wajen warware takaddama.

ADVERTISEMENT

Ba ma wai kawai matakin da Amurka da Isra’ila suka dauka na kaddamar da hare-hare a kan Iran haramtacce ne da ya yi karan-tsaye ga kundin Majalisar Dinkin Duniya ba, an dauke shi ne ana kan tattaunawar zaman lafiya. Bugu da kari, idan aka dubi hujjar nukiliya da aka bayar ta kai hare-haren, ita kanta Isra’ila da ta zama kanwa uwar-gamin abun, ba ta cikin kasashen da suka rattaba hannu kan haramcin makaman nukiliya a duniya. Kuma a tambayi hukumar IAEA mai kula da makamashin nukiliya ta duniya, shin ko a mafarki ta taba kai ziyara Isra’ila da nufin binciken sha’anin nukiliyar kasar?

Matukar ana son magance matsala da gaske, daga tushe ake tumbuke jijiyar musabbabinta, kuma wannan shi ne adalcin da kasar Sin ta nemi a yi wa kowane bangare na rikicin, domin idan ba a faro daga nan ba, zai zamo an kashe maciji ne amma ba a sare kansa ba.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A lokacin da Isra’ila take farko-farkon kaddamar da hare-harenta a zirin Gaza wadanda suka salwantar da dubban rayukan fararen hula, a wani tsokaci da ya yi, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce, ya kamata a duba matsalar daga tushe, ma’ana, mene ne ya haddasa harin da Hamas ta kai ranar 7 ga Oktobar 2023, domin kamar yadda ya ce, komin raunin mutum idan tura ta kai shi bango, zuciyarsa tana kekashewa. Amma me ya biyo bayan maganar tasa? Yekuwar a tumbuke shi daga kujerarsa ta MDD daga bangaren Isra’ila da wasu kawayenta, maimakon duba abin da idon basira.

A wata mukalar da ya taba rubutawa, masanin zamantakewar dan’adam, farfesan farfesoshi kan sulhunta rikicin kasa da kasa a Jami’ar Notre Dames, John Paul Lederach ya bayyana cewa, zaman lafiya mai dorewa yana samuwa ne daga magance rikici daga tushe. Shi ma masanin zamantakewa Johan Galtun a wata mukalarsa ya bayyana cewa, rikici yana kunno kai ne daga rashin adalci da daidaito.

A halin yanzu dai, kasar Sin ta haska hanya game da komawa turbar adalci a fagen kasa da kasa, kuma tambayar da mutane da dama ke yi ita ce, sai yaushe wasu kasashe za su warke daga makantarsu ta fadar gaskiya da adalci? (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sulhu
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sulhu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Maraba Da Shirin Tsagaita Wuta A Rikicin Iran

Kasar Sin Na Maraba Da Shirin Tsagaita Wuta A Rikicin Iran

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.