A ranar Litinin, Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da kudirin kasafin kudi na Naira tiriliyan 1.50 ga rundunar sojin Nijeriya na shekarar 2026, inda ta yi alkawarin goyon baya don tabbatar da fitar da kudaden akan lokaci.
Amincewar ta biyo bayan zaman hadin gwiwa na Kwamitin Majalisar Dattawa da na Wakilai, wanda ya gudana a Abuja, inda Babban Hafsan Soja, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya gabatar da cikakkun bayanai game da kasafin kudin da aka tsara na shekara mai zuwa.
Da yake jawabi bayan zaman, Shugaban Kwamitin Rundunar Soji na Majalisar Dattawa, Sanata Abdulaziz Yar’Adua, ya ce ‘yan majalisar sun gamsu da bayanan da aka gabatar kuma sun sake jaddada kudirinsu na tallafawa rundunar soji wajen gudanar da ayyukanta, wanda kundin tsarin mulki ya tanadar mata.
“Mun yi zaman hadin gwiwa na Kwamitocin Majalisar Dattawa da na Majalisar Wakilai kan Rundunar Soja kan kasafin kudi na 2026, kuma bayan sauraron gabatarwar da Babban Hafsan Sojan ya yi, dukkan ‘yan majalisar sun nuna gamsuwa da hakan,” In ji Sanata Yar’Adua.















Discussion about this post