Sanata Rabiu Kwankwaso, ɗan takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar NDC, ya ce gwamnonin da ke tunanin yin maguɗin zaɓe da kuma iko da tsarin gwamnati na jihohi domin ci gaba da riƙe muƙamansu bayan zaɓen 2027 za su kunyata.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) a Abuja ranar Lahadi.Tsohon Gwamnan Jihar Kano ya ce wasu gwamnonin da suka gaza magance matsalolin al’ummominsu na komawa jam’iyyar APC, bisa zargin cewa, siyasar jam’iyyar mai mulki zai taimaka musu wajen sake lashe zaɓe.
Ya ce ƙara nuna rashin gamsuwa da rashin tsaro, talauci, rashin aikin yi da kuma tabarbarewar ayyukan jama’a na iya yin tasiri sosai wajen yanke shawarar masu zaɓe a lokacin zaɓe.
A cewar Kwankwaso, ‘yan Nijeriya na ƙara wayewa a fannin siyasa, kuma hakan na iya sa su ƙi zaɓar gwamnonin da sauran ‘yan siyasar da ke neman ƙarin wa’adi, duk da cewa suna da iko da tsarin gwamnati.
“Abin da nake hasashe a zaɓen 2027 shi ne, yawancin gwamnonin da ke neman sake komawa kan kujerunsu za su kunyata, domin jama’a ba za su mara musu baya ba.” In ji Kwankwaso














