ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Ya Buƙaci Gwamnati Ta Haɗe Rundunar Tsaro Ta Jihohi Cikin Sojojin Nijeriya 

by Sulaiman
7 months ago

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta haɗe rundunar jami’an tsaro ta al’umma ta jihohi da aka ƙaddamar cikin jami’an tsaronta don ƙarfafa rundunonin sojoji da kuma magance matsalar rashin tsaro da ke ƙaruwa.

 

Kwankwaso ya yi wannan kiran ne a ranar Talata yayin bikin rantsar da mambobi 2,000 na Rundunar Tsaron Al’umma ta Jihar Kano.

ADVERTISEMENT
  • An Kaddamar Da Aikin Gyaran Babbar Hanyar Da Ta Hade Senegal Da Guinea-Bissau
  • ‘Yansanda Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Fashi A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa na 2023 a Jam’iyyar NNPP ya bayyana cewa, Nijeriya na buƙatar aƙalla ma’aikatan soja miliyan ɗaya don fuskantar ƙalubalen tsaro a faɗin ƙasar yadda ya kamata, yana mai jaddada cewa, akwai nuna rashin sanin muhimmancin tsaro daga shugabannin siyasa a matakin tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

“Abin da muka rasa shi ne himma daga shugabanninmu na siyasa, musamman Babban shugaban rundunar tsaron ƙasa da kansa,” in ji Kwankwaso. “Ya kamata ya tabbatar da cewa an sake horar da waɗannan sabbin jami’an, a basu kaki, da bindigu, da harsasai.”

 

Ya ƙara da cewa, ya kamata a haɗa ƙungiyoyin tsaro na sassan arewa da kudancin ƙasar cikin aikin soja don kawo ƙarshen abin da ya bayyana a matsayin “hauka da ke faruwa a wannan ƙasar.”

 

“Ina ba Gwamnatin Tarayya shawara da ta yi duk abin da za ta iya don ɗaukar waɗannan rundunonin a jihohi kamar Sokoto, Katsina, Kano da Zamfara. Wannan zai ƙara yawan jami’an tsaro a wannan ƙasar,” in ji Kwankwaso.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga sabuwar Rundunar Tsaron Al’umma da ta yi ƙoƙari na musamman don ƙarfafa wa ƙoƙarin hukumomin tsaro, musamman a yankunan kan iyaka da ke fuskantar barazanar tsaro.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
  • Sulaiman
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
  • Sulaiman
    Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa
  • Sulaiman
    Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Jimillar Tashoshin 5G Na Sin Ta Kai Miliyan 4.83

Jimillar Tashoshin 5G Na Sin Ta Kai Miliyan 4.83

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.