ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Ya Buƙaci Gwamnati Ta Haɗe Rundunar Tsaro Ta Jihohi Cikin Sojojin Nijeriya 

by Sulaiman
9 months ago

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma shugaban tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta haɗe rundunar jami’an tsaro ta al’umma ta jihohi da aka ƙaddamar cikin jami’an tsaronta don ƙarfafa rundunonin sojoji da kuma magance matsalar rashin tsaro da ke ƙaruwa.

 

Kwankwaso ya yi wannan kiran ne a ranar Talata yayin bikin rantsar da mambobi 2,000 na Rundunar Tsaron Al’umma ta Jihar Kano.

ADVERTISEMENT
  • An Kaddamar Da Aikin Gyaran Babbar Hanyar Da Ta Hade Senegal Da Guinea-Bissau
  • ‘Yansanda Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Fashi A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa na 2023 a Jam’iyyar NNPP ya bayyana cewa, Nijeriya na buƙatar aƙalla ma’aikatan soja miliyan ɗaya don fuskantar ƙalubalen tsaro a faɗin ƙasar yadda ya kamata, yana mai jaddada cewa, akwai nuna rashin sanin muhimmancin tsaro daga shugabannin siyasa a matakin tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

“Abin da muka rasa shi ne himma daga shugabanninmu na siyasa, musamman Babban shugaban rundunar tsaron ƙasa da kansa,” in ji Kwankwaso. “Ya kamata ya tabbatar da cewa an sake horar da waɗannan sabbin jami’an, a basu kaki, da bindigu, da harsasai.”

 

Ya ƙara da cewa, ya kamata a haɗa ƙungiyoyin tsaro na sassan arewa da kudancin ƙasar cikin aikin soja don kawo ƙarshen abin da ya bayyana a matsayin “hauka da ke faruwa a wannan ƙasar.”

 

“Ina ba Gwamnatin Tarayya shawara da ta yi duk abin da za ta iya don ɗaukar waɗannan rundunonin a jihohi kamar Sokoto, Katsina, Kano da Zamfara. Wannan zai ƙara yawan jami’an tsaro a wannan ƙasar,” in ji Kwankwaso.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga sabuwar Rundunar Tsaron Al’umma da ta yi ƙoƙari na musamman don ƙarfafa wa ƙoƙarin hukumomin tsaro, musamman a yankunan kan iyaka da ke fuskantar barazanar tsaro.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP
  • Sulaiman
    Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
  • Sulaiman
    Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
  • Sulaiman
    Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

MASU ALAKA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro
Manyan Labarai

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
Jimillar Tashoshin 5G Na Sin Ta Kai Miliyan 4.83

Jimillar Tashoshin 5G Na Sin Ta Kai Miliyan 4.83

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.