ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Ribas Ya Ba Da Tabbacin Kare ‘Yan Kasashen Waje A Jihar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) reshen Jihar Ribas, James Sunday, ya tabbatar wa ‘yan kasashen waje mazauna Nijeriya da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ke jihar, cewa su sha kuruminsu za a kare musu harkokin kasuwancinsu da hannun jarinsu gabanin da bayan zaben Nijeriya.

Da ya ke magana da ‘yan kasashen wajen ta kafar sadarwa, Kwanturolan ya jaddada kokarin da hukumar NIS ke yi wajen taimaka wa wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ‘yan kasashen waje da ke zaune a Nijeriya, ‘yan kasashen waje da ke nemin izinin aiki, neman izinin zama da yin kaura ta musamman (SIS).

  • NIS Ta Kama Wasu Mata 11 Da Aka Yi Fataucinsu Zuwa Kasar Libiya

 

ADVERTISEMENT

Kazalika da wadanda ba ‘yan Nijeriya ba (Maza) da ke neman auren mace ‘yar Nijeriya bayan cika dukkanin ka’idojin da hakan ke bukata da kuma wadanda suke gudanar da harkokin kasuwancinsu bisa doka da ka’ida tare da cikakken izini ko wasu da ke da wani aikin yi na musamman a cikin kasar nan.

Ya kara da cewa dukkanin wadannan rukunin mutanen (Yan kasan waje) da su kwantar da hankalinsu su ji kamar a gidajensu ko kasashensu na asali su ke domin cigaba da bunkasa harkokin kasuwanci.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

A cewar wata sanarwar daga sashin yada labarai na hukumar a jihar Ribas, James ya kuma bukaci ‘yan kasashen wajen da su cigaba da mutunta dokoki da ka’idojin Nijeriya da aka shimfida musu tare da bada wa ‘yan Nijeriya suke aiki da su domin rage matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa.

‘Yan kasashen waje mazauna Ribas sun samu tabbacin cewa za a basu cikakken kariya da harkokin kasuwancinsu muddin za su cigaba da mutunta dokoki da ka’idojin dukkanin hukumomin da suka shafi shige da fice da kuma zama halastaccen masu zuba hannun jari a Ribas da ma Nijeriya.

James Sunday ya kuma ba su tabbacin cewa kofar su a bude take wajen kyautatawa da inganta kyakkyawar alaka a tsakanin hukumar ta NIS da ‘yan kasashen waje domin bunkasa hada-hadar kasuwanci da zuba hannun jari.

  • https://leadership.ng/leadership-award-a-landmark-history-for-me-nis-cg-jere/
NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Tsohon Mai Horas Da ‘Yan Wasan Kwallon Kafa Na Falcons, Ismaila Mabo, Ya Rasu

Tsohon Mai Horas Da 'Yan Wasan Kwallon Kafa Na Falcons, Ismaila Mabo, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.