Wasu da ake zargin Lakurawa ne sun kashe jami’an Hukumar Kwastam ta Ƙasa guda biyu a garin Tuga da ke ƙaramar hukumar Bagudu a Jihar Kebbi.
Rahotanni sun ce harin ya auku ne da sanyin safiyar ranar Laraba lokacin da maharan suka kai hari wuraren binciken jami’an tsaro guda biyu da misalin ƙarfe 3 na dare.
Wata majiya ta ce maharan sun kai harin ba tare da jami’an sun yi tsammani ba.
An ce sun ƙone wani babban jami’i har lahira bayan sun banka wa wajen da yake hutawa wuta, yayin da suka harbe wani jami’in har lahir.
Sauran jami’ai biyu da suka samu raunukan harbin bindiga na samun kulawa a asibiti.
Majiyar ta ƙara da cewa maharan sun isa ne cikin wata mota da suka ɓuya wadda suka yi amfani da ita a matsayin motar dakon dabbobi domin kauce wa zargi.
Mai magana da yawun Hukumar Kwastam a Jihar Kebbi, Mustapha Mubarak, ya ce za su fitar da sanarwa bayan sun kammala tattara bayanai kan lamarin.
Shi ma kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Bashir Usman, ba a samu jin ta bakinsa ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.















Discussion about this post