Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a garin Lokoja ta soke hukuncin da ta yanke a baya na umartar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta yi rajistar jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) a matsayin jam’iyyar siyasa.
Wannan sabon hukunci da Mai Shari’a Isah Dashen ya yanke ya soke dukan matakan da aka ɗauka tun bayan umarnin farko, wanda hakan ke nufin an janye amincewa da jam’iyyar ta NDC na ɗan lokaci.
Kotun ta bayyana cewa hukuncinta na ranar 10 ga watan Disamba, 2025, ya tauye haƙƙoƙin jam’iyyar Peace Movement Party (PMP), wadda ba a haɗa ta a cikin shari’ar ba tun farko.
Jam’iyyar ta PMP ta nuna cewa tambarin (logo) da jam’iyyar NDC ta yi amfani da shi wajen samun nasara a kotu mallakarta ne na halal, kuma ta riga ta miƙa shi ga hukumar INEC tun kafin a fara shari’ar.
Sakamakon haka, kotun ta umarci dukan ɓangarorin da su koma matsayinsu na da kafin yanke hukuncin watan Disamban 2025, sannan ta umarci masu ƙara da su haɗa da dukan rukunonin da lamarin ya shafa domin a fuskanci shari’ar baki ɗaya.
Lauyan masu ƙorafin, C.S. Ekeocha, ya bayyana cewa dukan takaddun shaida, da rajista, da sanya sunan NDC a cikin jadawalin INEC ko takardun zaɓe za a janye su har sai an kammala ainihin shari’ar.
Duk da wannan soke hukunci, lauyan ya jaddada cewa ainihin shari’ar tana nan a gaban kotu kuma ba a gama yanke mata hukunci na ƙarshe ba.














