Mai magana da yawun majalisar bunkasa kasuwancin kasa da kasa ta kasar Sin, watau CCPIT a takaice, ya amsa tambayoyin wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, watau CMG a yau, dangane da ziyarar da wakilan ‘yan kasuwar Amurka, wadanda ke cikin babbar tawagar Amurka, suka kawo kasar Sin.
Mai magana da yawun ya bayyana cewa, majalisar CCPIT tana maraba da zuwan wakilan ‘yan kasuwar Amurka kasar Sin. Ya ce akwai sarari mai fadi da babbar dama ta yin hadin gwiwa mai ma’ana a tsakanin Sin da Amurka.
Ana sa ran cewa, karkashin kyakkyawan jagorancin shugabannin kasashen biyu, ‘yan kasuwar Sin da Amurka za su kara zurfafa mu’amala da hadin gwiwa, tare da bayar da sabbin gudummawa ga samun kyakkyawar dangantaka mai dorewa ba tare da tangarda ba a tsakanin Sin da Amurka. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post