ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogo Na TAZARA: Shaida Ce Ta Abota Da Ta Wuce Rabin Karni

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
TAZARA

Ranar 5 ga watan Afrilu ita ce ranar bikin gargajiya ta Sinawa na tunawa da magabata, wato bikin Qingming. A ranar ta wannan shekara, an gudanar da wani biki na musamman don tunawa da ma’aikata Sinawa da suka rasa rayukansu, yayin ginin layin dogo na TAZARA, wanda ya hada kasashen Tanzania da Zambia. David Robert, yaro dan kasar Tanzaniya mai shekaru 11 ya tsaya a gaban kaburburan kwararrun kasar Sin da suka sadaukar da rayukansu, ya kalli sunayen Sinawa da aka sassaka a kan dutsen kaburburan, ya ce: “Na karanta layin dogo na TAZARA a makaranta, malamina ya ce, ya kasance alama ta abota tsakanin Sin da Tanzaniya.”

Bikin ya tuna min da abin da ya faru lokacin da na yi ziyara a kasar Zambia a watan Fabrairun wannan shekara. Lokacin da na je wurin tunawa da layin dogo na TAZARA don karrama ma’aikata Sinawa da suka sadaukar da rayukansu wajen gina wannan layi, wadanda aka binne a can, na sadu da wani dalibi mai ziyara, wanda ya ce mini: “Mun koya a makaranta cewa, Sinawa ne suka taimaka mana wajen gina wannan layin dogo, wannan ita ce ‘hanyar abota’.” Ban sami damar tambayar sunansa ba, sai ya yi murmushi ya tafi, amma na san cewa yawancin yaran Zambia irinsa suna rike da abokantaka tsakanin Zambia da Sin a zukatansu.

Wata hasumiyar tunawa na tsaye a tsakiyar wurin tunawa da layin dogo na Tazara, tana wakiltar abota tsakanin kasashe uku na Sin da Tanzaniya da Zambia.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun 1970, bayan da kasashen yamma suka ki amincewa da bukatar Tanzaniya na gina mata layin dogo saboda “rashin fa’idar tattalin arziki”, dubban ma’aikata Sinawa sun tafi Afirka, inda suka yi aiki kafada da kafada da mutanen Tanzaniya da Zambia don gina layin dogo na TAZARA. Duk da yanayi mai zafi, cututtuka da karancin kayayyaki, sun kai ga shimfida wannan layin dogo da ya hada kasashen da ke nisa da teku da tashar ruwa.

Bayan kammala wannan layin dogo mai tsawon kilomita 1,860.5, ya samar da sabuwar hanyar fita zuwa teku ga Zambia da sauran kasashen Afirka da ke da nisa daga teku, ta yadda albarkatun kasashen sun zama karfin bunkasa tattalin arzikinsu, matakin da ya sa kasashen suka yi watsi da tarnakin da aka yi musu ta fannin tattalin arziki tare da samun ‘yanci na gaske. A lokacin gina shi, ma’aikata Sinawa 51 sun rasa rayukansu. Saboda hakan, ana kira layin dogon “hanyar ‘yanci” da “hanyar abota”.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

A bana ake cika shekara ta 50 da fara aiki da wannan layin dogo. A ranar 20 ga watan Nuwamban bara, an gudanar da bikin kaddamar da aikin sabunta wannan layin dogo a Lusaka na Zambia. A halin yanzu, kamfanin CCECC na kasar Sin yana jagorantar ayyukan gine-gine masu alaka.

A sabon mafari na tarihi, ba za a manta da jaruman da suka sadaukar da rayukansu wajen gina layin dogon ba, kuma abota tsakanin Sin, Tanzaniya da Zambia ba za ta dushe ba. Kamar yadda ministan harkokin cikin gida na Tanzaniya George Katambi ya fada a bikin tunawa: “Wadannan jarumai ba wani bangare na tarihi kadai ba ne, har ma wani bangare ne na makomarmu.” (Marubuci:MINA)

 

TAZARA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
TAZARA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana
  • Sulaiman
    Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD
  • Sulaiman
    Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani
  • Sulaiman
    Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026
Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

July 20, 2026
Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.