ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogo Na TAZARA: Shaida Ce Ta Abota Da Ta Wuce Rabin Karni

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
TAZARA

Ranar 5 ga watan Afrilu ita ce ranar bikin gargajiya ta Sinawa na tunawa da magabata, wato bikin Qingming. A ranar ta wannan shekara, an gudanar da wani biki na musamman don tunawa da ma’aikata Sinawa da suka rasa rayukansu, yayin ginin layin dogo na TAZARA, wanda ya hada kasashen Tanzania da Zambia. David Robert, yaro dan kasar Tanzaniya mai shekaru 11 ya tsaya a gaban kaburburan kwararrun kasar Sin da suka sadaukar da rayukansu, ya kalli sunayen Sinawa da aka sassaka a kan dutsen kaburburan, ya ce: “Na karanta layin dogo na TAZARA a makaranta, malamina ya ce, ya kasance alama ta abota tsakanin Sin da Tanzaniya.”

Bikin ya tuna min da abin da ya faru lokacin da na yi ziyara a kasar Zambia a watan Fabrairun wannan shekara. Lokacin da na je wurin tunawa da layin dogo na TAZARA don karrama ma’aikata Sinawa da suka sadaukar da rayukansu wajen gina wannan layi, wadanda aka binne a can, na sadu da wani dalibi mai ziyara, wanda ya ce mini: “Mun koya a makaranta cewa, Sinawa ne suka taimaka mana wajen gina wannan layin dogo, wannan ita ce ‘hanyar abota’.” Ban sami damar tambayar sunansa ba, sai ya yi murmushi ya tafi, amma na san cewa yawancin yaran Zambia irinsa suna rike da abokantaka tsakanin Zambia da Sin a zukatansu.

Wata hasumiyar tunawa na tsaye a tsakiyar wurin tunawa da layin dogo na Tazara, tana wakiltar abota tsakanin kasashe uku na Sin da Tanzaniya da Zambia.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun 1970, bayan da kasashen yamma suka ki amincewa da bukatar Tanzaniya na gina mata layin dogo saboda “rashin fa’idar tattalin arziki”, dubban ma’aikata Sinawa sun tafi Afirka, inda suka yi aiki kafada da kafada da mutanen Tanzaniya da Zambia don gina layin dogo na TAZARA. Duk da yanayi mai zafi, cututtuka da karancin kayayyaki, sun kai ga shimfida wannan layin dogo da ya hada kasashen da ke nisa da teku da tashar ruwa.

Bayan kammala wannan layin dogo mai tsawon kilomita 1,860.5, ya samar da sabuwar hanyar fita zuwa teku ga Zambia da sauran kasashen Afirka da ke da nisa daga teku, ta yadda albarkatun kasashen sun zama karfin bunkasa tattalin arzikinsu, matakin da ya sa kasashen suka yi watsi da tarnakin da aka yi musu ta fannin tattalin arziki tare da samun ‘yanci na gaske. A lokacin gina shi, ma’aikata Sinawa 51 sun rasa rayukansu. Saboda hakan, ana kira layin dogon “hanyar ‘yanci” da “hanyar abota”.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

A bana ake cika shekara ta 50 da fara aiki da wannan layin dogo. A ranar 20 ga watan Nuwamban bara, an gudanar da bikin kaddamar da aikin sabunta wannan layin dogo a Lusaka na Zambia. A halin yanzu, kamfanin CCECC na kasar Sin yana jagorantar ayyukan gine-gine masu alaka.

A sabon mafari na tarihi, ba za a manta da jaruman da suka sadaukar da rayukansu wajen gina layin dogon ba, kuma abota tsakanin Sin, Tanzaniya da Zambia ba za ta dushe ba. Kamar yadda ministan harkokin cikin gida na Tanzaniya George Katambi ya fada a bikin tunawa: “Wadannan jarumai ba wani bangare na tarihi kadai ba ne, har ma wani bangare ne na makomarmu.” (Marubuci:MINA)

 

TAZARA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
TAZARA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Next Post
Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.