ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogo Na TAZARA: Shaida Ce Ta Abota Da Ta Wuce Rabin Karni

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
TAZARA

Ranar 5 ga watan Afrilu ita ce ranar bikin gargajiya ta Sinawa na tunawa da magabata, wato bikin Qingming. A ranar ta wannan shekara, an gudanar da wani biki na musamman don tunawa da ma’aikata Sinawa da suka rasa rayukansu, yayin ginin layin dogo na TAZARA, wanda ya hada kasashen Tanzania da Zambia. David Robert, yaro dan kasar Tanzaniya mai shekaru 11 ya tsaya a gaban kaburburan kwararrun kasar Sin da suka sadaukar da rayukansu, ya kalli sunayen Sinawa da aka sassaka a kan dutsen kaburburan, ya ce: “Na karanta layin dogo na TAZARA a makaranta, malamina ya ce, ya kasance alama ta abota tsakanin Sin da Tanzaniya.”

Bikin ya tuna min da abin da ya faru lokacin da na yi ziyara a kasar Zambia a watan Fabrairun wannan shekara. Lokacin da na je wurin tunawa da layin dogo na TAZARA don karrama ma’aikata Sinawa da suka sadaukar da rayukansu wajen gina wannan layi, wadanda aka binne a can, na sadu da wani dalibi mai ziyara, wanda ya ce mini: “Mun koya a makaranta cewa, Sinawa ne suka taimaka mana wajen gina wannan layin dogo, wannan ita ce ‘hanyar abota’.” Ban sami damar tambayar sunansa ba, sai ya yi murmushi ya tafi, amma na san cewa yawancin yaran Zambia irinsa suna rike da abokantaka tsakanin Zambia da Sin a zukatansu.

Wata hasumiyar tunawa na tsaye a tsakiyar wurin tunawa da layin dogo na Tazara, tana wakiltar abota tsakanin kasashe uku na Sin da Tanzaniya da Zambia.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun 1970, bayan da kasashen yamma suka ki amincewa da bukatar Tanzaniya na gina mata layin dogo saboda “rashin fa’idar tattalin arziki”, dubban ma’aikata Sinawa sun tafi Afirka, inda suka yi aiki kafada da kafada da mutanen Tanzaniya da Zambia don gina layin dogo na TAZARA. Duk da yanayi mai zafi, cututtuka da karancin kayayyaki, sun kai ga shimfida wannan layin dogo da ya hada kasashen da ke nisa da teku da tashar ruwa.

Bayan kammala wannan layin dogo mai tsawon kilomita 1,860.5, ya samar da sabuwar hanyar fita zuwa teku ga Zambia da sauran kasashen Afirka da ke da nisa daga teku, ta yadda albarkatun kasashen sun zama karfin bunkasa tattalin arzikinsu, matakin da ya sa kasashen suka yi watsi da tarnakin da aka yi musu ta fannin tattalin arziki tare da samun ‘yanci na gaske. A lokacin gina shi, ma’aikata Sinawa 51 sun rasa rayukansu. Saboda hakan, ana kira layin dogon “hanyar ‘yanci” da “hanyar abota”.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A bana ake cika shekara ta 50 da fara aiki da wannan layin dogo. A ranar 20 ga watan Nuwamban bara, an gudanar da bikin kaddamar da aikin sabunta wannan layin dogo a Lusaka na Zambia. A halin yanzu, kamfanin CCECC na kasar Sin yana jagorantar ayyukan gine-gine masu alaka.

A sabon mafari na tarihi, ba za a manta da jaruman da suka sadaukar da rayukansu wajen gina layin dogon ba, kuma abota tsakanin Sin, Tanzaniya da Zambia ba za ta dushe ba. Kamar yadda ministan harkokin cikin gida na Tanzaniya George Katambi ya fada a bikin tunawa: “Wadannan jarumai ba wani bangare na tarihi kadai ba ne, har ma wani bangare ne na makomarmu.” (Marubuci:MINA)

 

TAZARA
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
TAZARA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

LABARAI MASU NASABA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.