Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na Jam’iyyar (ADC) ya yi watsi da bangarorin jam’iyyar da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da kuma Rabiu Bala Gombe ke jagoranta, inda ya bayyana su a matsayin waɗanda ba su da inganci a bisa tsarin doka.
Da yake ganawa da manema labarai bayan taron NEC da aka gudanar a Abuja ranar Talata, Shugaban jam’iyyar na Jihar Abia, Don Norman Obinna, ya ce bangarorin biyu sun kasa cika sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da ake buƙata domin jagoranci.
- Ɗimbin Magoya Bayan Jam’iyyun APC, NNPP Da PDP Sun Koma ADC A Jihar Jigawa
- 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya
Obinna ya bayyana cewa NEC, wanda ya ce ya ƙunshi shugabannin jihohi 20, ya nuna damuwa kan abin da ya kira tsoma bakin wasu mutane da ba su da cikakkiyar fahimta kan harkokin cikin gida na jam’iyyar.
Ya ce, “Mun kalli abin da ke faruwa cikin mamaki, yadda wasu ‘yan kaɗan, waɗanda ba su da cikakkiyar fahimta kan batutuwan jam’iyyar, suka riƙa ɗaukar matakai bisa son rai ba tare da tunani da ilimi ba.”
Kwamitin NEC ya kuma bayyana goyon bayansa ga matakin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, wato (INEC), ta ɗauka na ƙin amincewa da ikirarin shugabanci daga bangarorin David Mark da Bala Gombe.
Da yake ƙarin bayani, Obinna ya ce wa’adin tsohon Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Ralph Nwosu, ya ƙare ne tun watan Agustan 2022, amma ya ƙi sauka daga mukaminsa, lamarin da ya jawo jerin shari’o’i a kotu.
A cewarsa, wani hukunci da Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke a watan Disamban 2022 ya tabbatar da cewa wa’adin Nwosu ya ƙare, don haka dukkan matakan da ya ɗauka tare da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa ba su da inganci, kasancewar ba su samu amincewar NEC ba.
Ya ce, “Wa’adin Ralph Nwosu a matsayin Shugaban Ƙasa ya ƙare a watan Agustan 2022. Rashin saukarsa ne ya haifar da shari’o’i da dama. Hukuncin kotu na watan Disamba ya tabbatar da cewa wa’adinsa ya ƙare, kuma duk wani mataki da ya ɗauka bayan haka ba shi da inganci.”
Biyo bayan waɗannan abubuwa, NEC ya sanar da naɗa Kwamitin Ayyuka na Ƙasa na riƙo domin tafiyar da harkokin jam’iyyar har zuwa lokacin da za a gudanar da babban taron ƙasa.
Kwamitin ya naɗa Ogga Temitope Kingsley, shugaban jam’iyyar a Jihar Kogi, a matsayin Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo, yayin da aka naɗa Odion O. Kennedy daga Jihar Edo a matsayin Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo.
Kwamitin na riƙo, wanda ya ƙunshi mutum takwas daga cikin shugabannin jihohi, an ba shi wa’adin makonni biyu domin tafiyar da harkokin jam’iyyar tare da tabbatar da miƙa mulki cikin sauƙi ga sabon shugabancin da za a zaɓa.















Discussion about this post