ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

by Muhammad
3 months ago
ADC

Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na Jam’iyyar (ADC) ya yi watsi da bangarorin jam’iyyar da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da kuma Rabiu Bala Gombe ke jagoranta, inda ya bayyana su a matsayin waɗanda ba su da inganci a bisa tsarin doka.

Da yake ganawa da manema labarai bayan taron NEC da aka gudanar a Abuja ranar Talata, Shugaban jam’iyyar na Jihar Abia, Don Norman Obinna, ya ce bangarorin biyu sun kasa cika sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da ake buƙata domin jagoranci.

  • Ɗimbin Magoya Bayan Jam’iyyun APC, NNPP Da PDP Sun Koma ADC A Jihar Jigawa
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Obinna ya bayyana cewa NEC, wanda ya ce ya ƙunshi shugabannin jihohi 20, ya nuna damuwa kan abin da ya kira tsoma bakin wasu mutane da ba su da cikakkiyar fahimta kan harkokin cikin gida na jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Mun kalli abin da ke faruwa cikin mamaki, yadda wasu ‘yan kaɗan, waɗanda ba su da cikakkiyar fahimta kan batutuwan jam’iyyar, suka riƙa ɗaukar matakai bisa son rai ba tare da tunani da ilimi ba.”

Kwamitin NEC ya kuma bayyana goyon bayansa ga matakin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, wato (INEC), ta ɗauka na ƙin amincewa da ikirarin shugabanci daga bangarorin David Mark da Bala Gombe.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Da yake ƙarin bayani, Obinna ya ce wa’adin tsohon Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Ralph Nwosu, ya ƙare ne tun watan Agustan 2022, amma ya ƙi sauka daga mukaminsa, lamarin da ya jawo jerin shari’o’i a kotu.

A cewarsa, wani hukunci da Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke a watan Disamban 2022 ya tabbatar da cewa wa’adin Nwosu ya ƙare, don haka dukkan matakan da ya ɗauka tare da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa ba su da inganci, kasancewar ba su samu amincewar NEC ba.

Ya ce, “Wa’adin Ralph Nwosu a matsayin Shugaban Ƙasa ya ƙare a watan Agustan 2022. Rashin saukarsa ne ya haifar da shari’o’i da dama. Hukuncin kotu na watan Disamba ya tabbatar da cewa wa’adinsa ya ƙare, kuma duk wani mataki da ya ɗauka bayan haka ba shi da inganci.”

Biyo bayan waɗannan abubuwa, NEC ya sanar da naɗa Kwamitin Ayyuka na Ƙasa na riƙo domin tafiyar da harkokin jam’iyyar har zuwa lokacin da za a gudanar da babban taron ƙasa.

Kwamitin ya naɗa Ogga Temitope Kingsley, shugaban jam’iyyar a Jihar Kogi, a matsayin Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo, yayin da aka naɗa Odion O. Kennedy daga Jihar Edo a matsayin Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo.

Kwamitin na riƙo, wanda ya ƙunshi mutum takwas daga cikin shugabannin jihohi, an ba shi wa’adin makonni biyu domin tafiyar da harkokin jam’iyyar tare da tabbatar da miƙa mulki cikin sauƙi ga sabon shugabancin da za a zaɓa.

ADC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Next Post
Bangaren Sin Ya Yi Kira a Bai Wa Kasashe Masu Tasowa Muhimmanci Yayin Yi Wa MDD Kwaskwarima

Bangaren Sin Ya Yi Kira a Bai Wa Kasashe Masu Tasowa Muhimmanci Yayin Yi Wa MDD Kwaskwarima

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.