ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

by Muhammad
3 months ago
ADC

Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na Jam’iyyar (ADC) ya yi watsi da bangarorin jam’iyyar da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da kuma Rabiu Bala Gombe ke jagoranta, inda ya bayyana su a matsayin waɗanda ba su da inganci a bisa tsarin doka.

Da yake ganawa da manema labarai bayan taron NEC da aka gudanar a Abuja ranar Talata, Shugaban jam’iyyar na Jihar Abia, Don Norman Obinna, ya ce bangarorin biyu sun kasa cika sharuddan kundin tsarin mulkin jam’iyyar da ake buƙata domin jagoranci.

  • Ɗimbin Magoya Bayan Jam’iyyun APC, NNPP Da PDP Sun Koma ADC A Jihar Jigawa
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Obinna ya bayyana cewa NEC, wanda ya ce ya ƙunshi shugabannin jihohi 20, ya nuna damuwa kan abin da ya kira tsoma bakin wasu mutane da ba su da cikakkiyar fahimta kan harkokin cikin gida na jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Mun kalli abin da ke faruwa cikin mamaki, yadda wasu ‘yan kaɗan, waɗanda ba su da cikakkiyar fahimta kan batutuwan jam’iyyar, suka riƙa ɗaukar matakai bisa son rai ba tare da tunani da ilimi ba.”

Kwamitin NEC ya kuma bayyana goyon bayansa ga matakin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, wato (INEC), ta ɗauka na ƙin amincewa da ikirarin shugabanci daga bangarorin David Mark da Bala Gombe.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Da yake ƙarin bayani, Obinna ya ce wa’adin tsohon Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Ralph Nwosu, ya ƙare ne tun watan Agustan 2022, amma ya ƙi sauka daga mukaminsa, lamarin da ya jawo jerin shari’o’i a kotu.

A cewarsa, wani hukunci da Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke a watan Disamban 2022 ya tabbatar da cewa wa’adin Nwosu ya ƙare, don haka dukkan matakan da ya ɗauka tare da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa ba su da inganci, kasancewar ba su samu amincewar NEC ba.

Ya ce, “Wa’adin Ralph Nwosu a matsayin Shugaban Ƙasa ya ƙare a watan Agustan 2022. Rashin saukarsa ne ya haifar da shari’o’i da dama. Hukuncin kotu na watan Disamba ya tabbatar da cewa wa’adinsa ya ƙare, kuma duk wani mataki da ya ɗauka bayan haka ba shi da inganci.”

Biyo bayan waɗannan abubuwa, NEC ya sanar da naɗa Kwamitin Ayyuka na Ƙasa na riƙo domin tafiyar da harkokin jam’iyyar har zuwa lokacin da za a gudanar da babban taron ƙasa.

Kwamitin ya naɗa Ogga Temitope Kingsley, shugaban jam’iyyar a Jihar Kogi, a matsayin Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo, yayin da aka naɗa Odion O. Kennedy daga Jihar Edo a matsayin Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa na riƙo.

Kwamitin na riƙo, wanda ya ƙunshi mutum takwas daga cikin shugabannin jihohi, an ba shi wa’adin makonni biyu domin tafiyar da harkokin jam’iyyar tare da tabbatar da miƙa mulki cikin sauƙi ga sabon shugabancin da za a zaɓa.

ADC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Bangaren Sin Ya Yi Kira a Bai Wa Kasashe Masu Tasowa Muhimmanci Yayin Yi Wa MDD Kwaskwarima

Bangaren Sin Ya Yi Kira a Bai Wa Kasashe Masu Tasowa Muhimmanci Yayin Yi Wa MDD Kwaskwarima

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.