• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Ra’ayin Blinken Kan Batun “Tarkon Bashi Na Kasar Sin”

by CMG Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Ra’ayin Blinken Kan Batun “Tarkon Bashi Na Kasar Sin”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin ziyarar da ya kai kasashen Afirka a kwanan nan, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken, ya sake yin tsokaci kan batun “tarkon bashi na kasar Sin”.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya musanta wannan batu a yayin taron manema labarai da aka saba shiryawa Alhamis din nan.

  • Sin: Babu Shakka Mahawarar MDD Game Da Kawar Da Wariyar Launin Fata Ta Aike Da Sako Ga Amurka

Yana mai cewa, batun “tarkon bashi na kasar Sin” karya ce da kasar Amurka da kasashen yammacin duniya suka kirkira, don kaucewa nauyin da ya rataya a wuyansu, wanda ba kowa ne ya yarda da shi ba. Don haka, ya dace su bar gaskiya ta bayyana kanta.

Wang ya ce, bashin da kasashe masu tasowa suka dauki dogon lokaci suna biya, galibi ya shafi masu lamuni na kasuwancin yammacin duniya da kuma cibiyoyi daban-daban.

Bankin duniya ya yi kiyasin cewa, kasashe masu karamin karfi da matsakaita, za su biya bashin dala biliyan 940 a cikin shekaru bakwai masu zuwa. Kuma daga cikin wannan adadi, kaso 67 cikin 100 ana biyansu ne ga masu ba da lamuni na kasuwanci na yammacin duniya da cibiyoyi da dama, Kudaden da ake biyan gwamnatin kasar Sin da cibiyoyin kasuwancin kasar, kashi 14 ne cikin 100 kawai.

Labarai Masu Nasaba

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

Wang ya yi nuni da cewa, kasar Sin ita ce ke kan gaba wajen ba da gudummawa ga ci gaba da aiwatar da shirin rage basussuka na kungiyar G20.

Sabanin haka, masu ba da lamuni na kasuwanci na yammacin duniya da cibiyoyi daban-daban, sun ki shiga ayyukan yafe basussuka, bisa la’akari da kare martabar lamunin da suka bayar, kuma ba su ba da gudummawar kwatankwacin na kasar Sin ba don sassauta nauyin bashin dake kan kasashe masu tasowa.(Ibrahim)

 

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abinda Ya Sa NNPP Ba Za Ta Iya Biya Wa Bangaren Shekarau Bukatunsa Ba – Kwankwaso

Next Post

Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Related

Hangzhou
Daga Birnin Sin

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

10 hours ago
Syria
Daga Birnin Sin

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

11 hours ago
Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

12 hours ago
Amurka
Daga Birnin Sin

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

14 hours ago
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 
Daga Birnin Sin

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

1 day ago
Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

1 day ago
Next Post
Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.