ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Rani: Gwamna Lawal Ya Raba Takin Zamani Da Kayan Noma Ga Manoman Jihar Zamfara

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran muhimman kayan noma domin tallafa wa manoma a kakar noman rani a faɗin jihar.

 

An ƙaddamar da shirin ne a ranar Alhamis a cibiyar Fadama III da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Noma ta jihar a Gusau.

ADVERTISEMENT

 

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, kayayyakin da aka raba suna da matuƙar muhimmanci wajen ƙara yawan amfanin gona, rage asarar da ake yi bayan girbi, da kuma bunƙasa noma mai ɗorewa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

 

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhunan takin NPK 3,920, buhunan takin Urea 1,956, litar maganin kashe ciyawa 3,920, litar maganin kashe ƙwari 1,956, da kuma fakitin maganin shafa iri 3,920.

 

An tsara rabon ne domin kaiwa ga manoma a sassa daban-daban na jihar, musamman ƙananan manoma da ke dogaro da noma a matsayin hanyar samun abinci da kuɗin shiga.

 

A jawabinsa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa shirin na daga cikin matakan da gwamnatinsa ke ɗauka domin ƙara yawan noma, inganta tsaron abinci da kuma bunƙasa rayuwar al’umma.

 

Ya ce noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin jihar, don haka wajibi ne gwamnati ta samar wa manoma kayan aikin da za su taimaka musu su yi noma cikin inganci.

 

Ya bayyana cewa shirye-shiryen NG-CARES sun samar da tubalin da ya bai wa gwamnatin jihar damar cimma nasarori a bangaren noma, musamman ta hanyar tallafa wa dubban ƙananan manoma da iri masu inganci, magungunan gona da shawarwarin dabarun noma.

 

Gwamnan ya yi kira ga manoman Zamfara da su yi amfani da kayayyakin da aka ba su yadda ya kamata, domin cimma manufar bunƙasa noma mai ɗorewa.

 

Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da amfani da irin waɗannan shirye-shirye wajen ƙara samar da abinci a cikin gida da rage dogaro da shigo da kayayyakin abinci daga ƙasashen waje.

 

Dangane da matsalolin tsaro, Gwamna Lawal ya amince cewa ƙalubalen tsaro na daga cikin manyan matsalolin da ke addabar noma a halin yanzu. Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa tsarin tsaro a yankunan karkara domin manoma su samu damar komawa gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

 

Haka kuma, ya yaba da goyon bayan da Gwamnatin Tarayya da abokan hulɗa na ci gaba ke bayarwa wajen aiwatar da shirin NG-CARES, yana mai cewa haɗin gwiwa tsakanin bangarori ne kaɗai zai tabbatar da nasarar manufofin ci gaban noma da tattalin arziki a jihar.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.