ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Rani: Gwamna Lawal Ya Raba Takin Zamani Da Kayan Noma Ga Manoman Jihar Zamfara

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran muhimman kayan noma domin tallafa wa manoma a kakar noman rani a faɗin jihar.

 

An ƙaddamar da shirin ne a ranar Alhamis a cibiyar Fadama III da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Noma ta jihar a Gusau.

ADVERTISEMENT

 

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, kayayyakin da aka raba suna da matuƙar muhimmanci wajen ƙara yawan amfanin gona, rage asarar da ake yi bayan girbi, da kuma bunƙasa noma mai ɗorewa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

 

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhunan takin NPK 3,920, buhunan takin Urea 1,956, litar maganin kashe ciyawa 3,920, litar maganin kashe ƙwari 1,956, da kuma fakitin maganin shafa iri 3,920.

 

An tsara rabon ne domin kaiwa ga manoma a sassa daban-daban na jihar, musamman ƙananan manoma da ke dogaro da noma a matsayin hanyar samun abinci da kuɗin shiga.

 

A jawabinsa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa shirin na daga cikin matakan da gwamnatinsa ke ɗauka domin ƙara yawan noma, inganta tsaron abinci da kuma bunƙasa rayuwar al’umma.

 

Ya ce noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin jihar, don haka wajibi ne gwamnati ta samar wa manoma kayan aikin da za su taimaka musu su yi noma cikin inganci.

 

Ya bayyana cewa shirye-shiryen NG-CARES sun samar da tubalin da ya bai wa gwamnatin jihar damar cimma nasarori a bangaren noma, musamman ta hanyar tallafa wa dubban ƙananan manoma da iri masu inganci, magungunan gona da shawarwarin dabarun noma.

 

Gwamnan ya yi kira ga manoman Zamfara da su yi amfani da kayayyakin da aka ba su yadda ya kamata, domin cimma manufar bunƙasa noma mai ɗorewa.

 

Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da amfani da irin waɗannan shirye-shirye wajen ƙara samar da abinci a cikin gida da rage dogaro da shigo da kayayyakin abinci daga ƙasashen waje.

 

Dangane da matsalolin tsaro, Gwamna Lawal ya amince cewa ƙalubalen tsaro na daga cikin manyan matsalolin da ke addabar noma a halin yanzu. Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa tsarin tsaro a yankunan karkara domin manoma su samu damar komawa gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

 

Haka kuma, ya yaba da goyon bayan da Gwamnatin Tarayya da abokan hulɗa na ci gaba ke bayarwa wajen aiwatar da shirin NG-CARES, yana mai cewa haɗin gwiwa tsakanin bangarori ne kaɗai zai tabbatar da nasarar manufofin ci gaban noma da tattalin arziki a jihar.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Sulaiman
    Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.