ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Da Ta Wakilai Sun Yi Alhinin Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
Majalisa

A ranar Talata, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ya jagoranci tawagar Majalisar dattawa domin miƙa ta’aziyya bisa rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Dahiru Usman Bauchi, bayan gabatar da ƙuduri na musamman a zauren Majalisar domin karrama Shaikh Dahiru da yaba wa irin gudunmawar da ya bayar a lokacin da ya ke raye.

 

Kazalika, shi ma Kakakin Majalisar Wakilai na tarayya Hon. Tajudden Abbas ya jagoranci tawagar ‘yan majalisar wakilai a wajen ta’aziyyar wanda ya gudana a Masallacin marigayin da ke unguwar Makera a cikin garin Bauchi. Mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Muhammad Auwal Jatau ne ya amshi tawagar.

ADVERTISEMENT
  • An Yi Taron Tattaunawa Kan Littafi Na 5 Na Xi Jinping Kan Dabarun Shugabanci A Kenya
  • ASUU Ta Yi Nasarar Cimma Manyan Buƙatunta Na Yarjejeniyar 2009 Da Gwamnati

Da su ke miƙa ta’aziyyar, Sanata Barau ya bayyana cewar rasuwar Sheikh Dahiru babban rashi ne da Nijeriya da ma Afrika suka yi, ya ce dukkanninsu sun ji matuƙar zafin rashin babban Malamin wanda ya zama uba, jagora kuma hadimin addinin Musulunci.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ce a zaman majalisar na ranar Talata ta gabatar da wani ƙudiri na musamman wanda dukkanin sanatoci suka yi alhini da juyayin rasuwar Shaikh Dahiru Usman Bauchi, “Dukkanin Sanatoci ba kawai zallar musulmai ba har da Kiristocin cikinmu kowa ya nuna irin babban rashin da aka yi, da jinjina masa kan hidimar da yayin wa addinin musulunci da bayar da gudummawarsa wajen kyautata zaman lafiya da haɗin kai a ƙasar nan.”

 

“Mun zo ne a madadin majalisar dattawa a bisa ƙudirin musamman da aka gabatar, don haka muna jajanta wa gwamnatin jihar Bauchi, iyalai, al’ummar jihar da Musulmai baki ɗaya.”

 

Ya ce rashin Shaikh Dahiru rashi ne da duniya ta yi, “Ayyukan da Shaikh Dahiru ya yi sun wuce Nijeriya, sun wuce maganar Afrika, yana daga cikin malaman da ake ji da su a duniya baki ɗaya.”

 

Barau ya yi addu’ar Allah ya jiƙansa ya gafarta masa. Sannan ya nemi iyalansa da su ya ƙoƙarin koyi da kyawawan ɗabi’u na mahaifinsu.

 

Tawagar majalisar dattijai ta haɗa da Sanata Sani Musa, shugaban kwamitin kuɗi; Sanata Muttati Dan Dutse, shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da manyan makarantu; Sanata Shehu Buba Umar, Sanata mai wakiltar Bauchi ta Kudu kuma shugaban kwamitin majalisar dattawa kan kiwo; Sanata Abdul’aziz Yar’adua, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sojoji; da hamshaƙin ɗan kasuwar mai Jack Rich, shi ma ya shiga tawagar majalisar dattawa.

 

Ɗaya daga cikin ‘ya’yan magayin, Dr. Bashir Dahiru Bauchi, ya gode wa tawagar Majalisar Dattawan bisa ziyarar da jajantawa.

 

A ɓangaren kakakin majalisar wakilai kuwa, Hon. Tajudden Abbas ya ce sun zo ne domin su wakilci dukkanin ‘yan majalisun tarayya su 360 domin miƙa ta’aziyyarsu bisa wannan babban rashin da Nijeriya ta yi.

 

“Wannan rashin ba rashi ne na mutanen Bauchi ba, ba rashi ne na Nijeriya ba, kima da ɗaukaka na Malam Dahiru ya zama na duniya ba ma Afrika ko Nijeriya ba; duk wani malami mai amsa sunan malamanta ya san ɗaukaka da irin rayuwa da babbanmu, kakanmu Malam Dahiru ya yi a tsawon rayuwarsa na hidima wa addini a wannan ƙasar.”

 

Ya ce yawan ɗalibai da Shaikh ɗin ya koyar sun ce a ce Nijeriya ne kaɗai don haka ya ce rashin ke na duniya. Sun miƙa ta’aziyyarsu wa gwamnatin Bauchi, Sarkin Bauchi, iyalai da ma jama’a Bauchi.

 

Daga cikin tawagar Majalisar wakilai akwai shugaban mai tsawatarwa na majalisar, Hon. Usman Bello Kumo; shugaban kwamitin kasafi, Hon. Abubakar Kabir Bichi; shugaban kwamitin harkokin mai, Hon. Alhassan Ado Doguwa; mataimakin shugaban marasa rinjaye, Aliyu Sani Madaki; shugaban kwamitin kula da harkokin tashoshin ruwa, Hon. Nnolim Nnaji da dai sauransu.

 

Sai kuma ‘yan majalisar tarayya daga Bauchi kamar su Bappa Aliyu Misau, Ali Garu da dai sauransu.

 

Ɗaya daga cikin ‘ya’yan marigayin Alhaji Surumbai Sheikh Dahiru Bauchi ne ya yi jawabin godiya a madadin iyalai, inda ya ce wa ‘yan majalisun dokokin wannan rashin gaba daya ne aka yi, don haka ya ce sun gode da ziyarar.

 

Wakilinmu ya labarto cewa ana ta kan ci gaba da amsar ta’aziyyar rasuwar malamin wanda ya rasu a ranar Alhamis. Tawagar daga sassan Nijeriya da ma ƙasashen Afrika ne ke ta zuwa domin mika ta’aziyyarsu.

Majalisa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Majalisar Dattawa Za Ta Tantance Sabon Ministan Tsaro Ranar Laraba

Majalisar Dattawa Za Ta Tantance Sabon Ministan Tsaro Ranar Laraba

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.