ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a

Zalunci ba zai dore ba - Natasha

by Sulaiman
1 year ago
Natasha

Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta tsakiya na tsawon watanni shida, daga ranar 6 ga Maris, 2025, bisa zarge-zargen rashin da’a da kuma saba dokokin majalisar dattawa (wacce aka yi wa kwaskwarima a 2023)

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, rikicin da ya kai ga dakatar da ita ya samo asali ne tun a watan Fabrairun da ya gabata lokacin da takaddamar sauya kujerar zama a zauren majalisar ta yi sanadin cacar baki tsakanin Sanata Akpoti-Uduaghan da Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio. Rikicin dai ya rikide zuwa zarge-zargen rashin da’a, lamarin da ya haifar da damuwa game da tsarin majalisar. Sai dai Akpabio ya musanta aikata laifin cin zarafin Sanatar, inda ya bayyana a ranar Laraba cewa “bai taba cin zarafin wata mace ba.”

ADVERTISEMENT
  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Idan Kunne Ya Ji, Jiki Ya Tsira

A zamanta na ranar Alhamis, kwamitin majalisar dattijai mai kula da da’a, gata, da sauraron kararrakin jama’a, karkashin jagorancin Sanata Neda Imasuen, ya gabatar da sakamakonsa, inda ya bayar da shawarwari guda bakwai. A cewar kwamitin, Akpoti-Uduaghan ta gaza bin dokokin majalisar dattawa sannan kuma ta yi watsi da kwamitin ta hanyar kin amsa gayyatar da ya yi mata.

 

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Don haka, Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida saboda saba ka’idojinta na majalisar dattawa.

 

Bugu da kari, majalisar ta bukaci Natasha da ta maido da duk wani abu mallakin majalisar ga mai kula da Majalisar har sai lokacin dakatarwar ya cika.

 

Sanata Imasuen ya bayyana cewa, “A madadin kwamitin majalisar dattawa kan da’a, gata, da kuma sauraron kararrakin jama’a, muna godiya ga shugaban kasa da manyan abokan aikinmu bisa damar da aka ba mu na yi wa ‘yan Nijeriya hidima ta hanyar wannan kwamiti. Mun gabatar da shawarwarinmu cikin girmamawa don tantancewa da amincewa. Na gode.”

 

Bayan doguwar muhawara kan rahoton da kwamitin ya gabatar, Sanatocin sun amince da dukkan shawarwarin ta hanyar kada kuri’a tare da yin kwaskwarima ga shawara ta 6, inda aka bai wa mataimakan Sanata Natasha damar karbar albashi da alawus-alawus din su domin kada su tagayyara.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, dukkan Sanatocin da suka yi magana sun nuna goyon bayansu ga sakamakon binciken.

 

A yayin da Sanatocin suka amince da shawarwarin, Sanata Natasha ta yi tsinkaye kan zaman, inda ta ce zalincin da aka yi mata ba zai dore ba. Daga nan aka fito da ita daga dakin zauren majalisar.

Natasha
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya

Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.