ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Dodo

A ranar 3 ga wata, gwamnatin kasar Amurka ta sanar da sanya karin haraji na kaso 10% a kan kayayyakin da take shigowa daga kasar Sin, biyowa bayan haraji na kaso 10% da ta kakaba wa kasar a watan da ya gabata. A wannan ranar, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya kuma tabbatar da fara aiki da matakan da a baya ya sanar na sanya karin haraji na kaso 25% a kan kayayyakin da take shigowa daga kasashen Mexico da Canada a ranar 4 ga wata. Sai dai sakamakon haka, babban mizanin wasu muhimman hannayen jari ya sauka matuka a kasuwar hannayen jari na Amurka, ciki har da DJIA da SPX da kuma IXIC, a yayin da mizanin VIX da ke auna yanayin damuwa da tashin hankali a Wallstreet ya yi tashin kwauron zabi. 

Shugaba Donald Trump kullum yana kallon haraji a matsayin matakin da zai iya tilasta wa kamfanoni maido da masana’antunsu cikin Amurka, don farfado da masana’antu da ma samar da guraben ayyuka a cikin gida. Sai dai in mun yi la’akari da abubuwan da suka faru a wa’adin shugabancinsa na farko, za mu gano cewa, bai ci burinsa ba. Dalilin hakan kuma shi ne Trump ya wuce gona da iri kan kintacen tasirin da karin haraji zai yi. Dunkulewar tattalin arzikin duniya bayan yakin duniya na biyu, ta sa akasarin masana’antu sun barbazu a sassan duniya daban daban, ga shi kuma fasahohi da ilmi da ma ababen sufuri da sauransu sun kasance tushen masana’antu na zamani, wadanda ke bukatar a shafe shekaru gommai wajen raya su. Don haka, matakan haraji ba za su iya kawar da matsalolin tushe na dakushewar masana’antu a kasar Amurka, a maimakon haka kuma, za su kara kudin da kamfanonin kasar suke kashewa da ma kudin da al’ummar kasar ke biya, wanda hakan zai kara tsananta matsalar hauhawar farashin a cikin gidan kasar.

  • Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su 
  • Ƴar Majalisar Dattawa Natasha Akpoti Na Fuskantar Dakatarwar Wata Shida

Kafofin yada labarai da dama na cikin gidan Amurka ma sun bayyana damuwarsu game da illolin da matakan haraji ka iya haifarwa. Kafar CNN ta ce, matakan haraji na cusa karin matsaloli ga tattalin arzikin kasar. Ta ce, matakan haraji za su kara kudin da al’ummar kasar ke biya, tare da kara matsawa kamfanonin kasar, wadanda ke fuskantar karin kudin da za su kashe da ma daina odar kayayyakinsu daga ketare.

ADVERTISEMENT

Bayan da Amurka ta sanar da sanya karin haraji, kasashen Canada da Mexico da ma Sin dukkan sun dauki matakan ramuwar gayya. A ranar 4 ga wata, bi da bi ne ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin da ma kwamitin kula da dokokin harajin kwastan na majalisar gudanarwar kasar sun sanar da jerin matakai na tinkarar matakan haraji na Amurka. Kakakin ma’aikatar wajen kasar Sin ya kuma jaddada cewa, nuna fin karfi ba shi da amfani da kasar Sin, kuma matsawa da barazana ba hanya ce ta cudanya da kasar. Hakikanin abubuwan da suka faru a shekarun baya ma sun shaida yadda kasar Sin ke mai da matsawa da aka yi mata a matsayin karfin da ke sa ci gabanta, bisa ga juriyar masana’antunta da kirkire-kirkiren fasahohi da ma hadin gwiwarta da sassa daban daban, har ma ta yi ta murkushe makircin Amurka.

A hakika, al’ummar kasar Amurka suna sane da me matakan haraji da Trump ya dauka za su haifar musu. Kamar yadda wani dan kasar ya ce, “idan an samu hauhawar farashi na kaso 25%, mu kanmu ne za mu biya kudin, a maimakon gwamnati ko mutanen kasar Mexico.” Abin hakan yake, duk da cewa matakin haraji ya lalata dokokin cinikin kasa da kasa tare da haifar da rashin tabbas ga farfadowar tattalin arzikin duniya, amma daga karshe, kamfanonin kasar Amurka da ma al’ummar kasar ne za su dandana kudarsa. Daidai kamar yadda Ben Ayers, masanin ilmin tattalin arziki na kasar Amurka ya ce, “Karin iyalai a Amurka za su kara kimtsa wa shiga yanayin tattalin arziki mara tabbas da za su fuskanta a shekarar 2025.”

LABARAI MASU NASABA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

 

Dodo
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Dodo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa
Ra'ayi Riga

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Next Post
Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da'a

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.