ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Yafe Harajin Kwastam Ga Afirka: Alfanun Abin Ya Zarce Batun Cinikayya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, kasar Sin za ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da suke sayarwa a kasuwanninta. Dangane da manufar, Babajide Tella, wani malami na jami’ar Howard ta kasar Amurka ya yi tsokaci, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria a kwanan baya.

A cewar Mista Tella, manufar nan ta kasar Sin, da farko dai, ta ba kasashen Afirka damammakin shigar da kayayyakinsu cikin kasuwannin Sin. Za a iya sayar da amfanin gona da sauran kayayyakin da aka kera a nahiyar Afirka a kasar Sin, wadda ke da yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4, ba tare da biyan harajin kwastam ko kwabo ba. Hakan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin daidaita yanayin cinikin da take yi tare da kasashen Afirka.

Ban da haka, Mista Tella ya ambaci yadda manufar Sin ta yafe harajin kwastam za ta amfani kasashen Afirka a kokarinsu na raya masana’antu. A cewarsa, tun daga lokacin mulkin mallaka har zuwa yanzu, kasashen Afirka sun dade suna fitar da danyun kayayyaki, da shigar da kayayyakin masana’antu da aka sarrafa daga sauran kasashe, lamarin da ya sa su rashin samun damar adana kudi. Sai dai sabuwar manufar kasar Sin ta yafe harajin kwastam za ta karfafa wa ‘yan kasuwa gwiwa domin a sarrafa danyun kayayyaki a kasashen Afirka kafin a fitar da su, da zummar daga darajar kayayyakin a kasuwannin kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Babajide Tella ya ce manufar kasar Sin ta amfanar da kasashen Afirka ta sa kaimi ga kasashen yamma domin su daidaita manufofinsu masu alaka da nahiyar Afirka. A cewarsa, kasashen yamma na ganin cewa, matakin kasar Sin na yafe harajin kwastam zai ba kasar damar samar da karin tasiri a nahiyar Afirka. Saboda haka, kasashen yamma suna kokarin daidaita manufofinsu da suka shafi nahiyar Afirka don kara janyo hankulan kasashen Afirka, da zummar takara da kasar Sin.

To, bayan karanta bayanin da Mista Babajide Tella ya rubata, ina so in ce, na yarda da yawancin ra’ayoyinsa. Sai dai na ga kamar bai samu cikakkiyar fahimtar dalilin da ya sa kasar Sin ta kuduri aniyar yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam ba. Sau da dama ya ambaci yadda kasar Sin ke “yin tasiri”, tamkar dai abun da kasar Sin ke nema daya ne da na kasashen yamma. Amma a hakika, ainihin dalilin da ya sa kasar Sin daukar mataki na amfanar da kasashen Afirka shi ne burin kasar na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

A ganin kasar Sin, mabambantan kasashe da al’ummu suna bukatar kasancewa tare da juna a duniyarmu. Saboda haka, a lokacin da wata kasa ke neman habaka moriyar kanta, ya kamata ta lura da damuwar sauran kasashe, da ba kasashe daban daban damar samun ci gaba na bai daya. Wannan tunani ya sa kasar Sin kullum take neman kulla huldar hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna tare da sauran kasashe, maimakon matakan cin moriya da faduwar wani da wasu kasashen yamma suka saba daukawa.

Wannan tunani ne ma ya sa kasar Sin bude kasuwanninta ga kasashen Afirka, a lokacin da wasu manyan kasashe ke kokarin saka shingayen ciniki. Hakika matakin yafe harajin kwastam da kasar Sin ke dauka a wannan karo ya riga ya zarce tsarin ciniki da na tattalin arziki, inda ya zamanto misalin yadda kasar Sin ke kokarin samar da gudunmowa wajen gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
  • Sulaiman
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.