ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Yafe Harajin Kwastam Ga Afirka: Alfanun Abin Ya Zarce Batun Cinikayya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, kasar Sin za ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da suke sayarwa a kasuwanninta. Dangane da manufar, Babajide Tella, wani malami na jami’ar Howard ta kasar Amurka ya yi tsokaci, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria a kwanan baya.

A cewar Mista Tella, manufar nan ta kasar Sin, da farko dai, ta ba kasashen Afirka damammakin shigar da kayayyakinsu cikin kasuwannin Sin. Za a iya sayar da amfanin gona da sauran kayayyakin da aka kera a nahiyar Afirka a kasar Sin, wadda ke da yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4, ba tare da biyan harajin kwastam ko kwabo ba. Hakan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin daidaita yanayin cinikin da take yi tare da kasashen Afirka.

Ban da haka, Mista Tella ya ambaci yadda manufar Sin ta yafe harajin kwastam za ta amfani kasashen Afirka a kokarinsu na raya masana’antu. A cewarsa, tun daga lokacin mulkin mallaka har zuwa yanzu, kasashen Afirka sun dade suna fitar da danyun kayayyaki, da shigar da kayayyakin masana’antu da aka sarrafa daga sauran kasashe, lamarin da ya sa su rashin samun damar adana kudi. Sai dai sabuwar manufar kasar Sin ta yafe harajin kwastam za ta karfafa wa ‘yan kasuwa gwiwa domin a sarrafa danyun kayayyaki a kasashen Afirka kafin a fitar da su, da zummar daga darajar kayayyakin a kasuwannin kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Babajide Tella ya ce manufar kasar Sin ta amfanar da kasashen Afirka ta sa kaimi ga kasashen yamma domin su daidaita manufofinsu masu alaka da nahiyar Afirka. A cewarsa, kasashen yamma na ganin cewa, matakin kasar Sin na yafe harajin kwastam zai ba kasar damar samar da karin tasiri a nahiyar Afirka. Saboda haka, kasashen yamma suna kokarin daidaita manufofinsu da suka shafi nahiyar Afirka don kara janyo hankulan kasashen Afirka, da zummar takara da kasar Sin.

To, bayan karanta bayanin da Mista Babajide Tella ya rubata, ina so in ce, na yarda da yawancin ra’ayoyinsa. Sai dai na ga kamar bai samu cikakkiyar fahimtar dalilin da ya sa kasar Sin ta kuduri aniyar yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam ba. Sau da dama ya ambaci yadda kasar Sin ke “yin tasiri”, tamkar dai abun da kasar Sin ke nema daya ne da na kasashen yamma. Amma a hakika, ainihin dalilin da ya sa kasar Sin daukar mataki na amfanar da kasashen Afirka shi ne burin kasar na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A ganin kasar Sin, mabambantan kasashe da al’ummu suna bukatar kasancewa tare da juna a duniyarmu. Saboda haka, a lokacin da wata kasa ke neman habaka moriyar kanta, ya kamata ta lura da damuwar sauran kasashe, da ba kasashe daban daban damar samun ci gaba na bai daya. Wannan tunani ya sa kasar Sin kullum take neman kulla huldar hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna tare da sauran kasashe, maimakon matakan cin moriya da faduwar wani da wasu kasashen yamma suka saba daukawa.

Wannan tunani ne ma ya sa kasar Sin bude kasuwanninta ga kasashen Afirka, a lokacin da wasu manyan kasashe ke kokarin saka shingayen ciniki. Hakika matakin yafe harajin kwastam da kasar Sin ke dauka a wannan karo ya riga ya zarce tsarin ciniki da na tattalin arziki, inda ya zamanto misalin yadda kasar Sin ke kokarin samar da gudunmowa wajen gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.