Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, kasar Sin za ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da suke sayarwa a kasuwanninta. Dangane da manufar, Babajide Tella, wani malami na jami’ar Howard ta kasar Amurka ya yi tsokaci, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria a kwanan baya.
A cewar Mista Tella, manufar nan ta kasar Sin, da farko dai, ta ba kasashen Afirka damammakin shigar da kayayyakinsu cikin kasuwannin Sin. Za a iya sayar da amfanin gona da sauran kayayyakin da aka kera a nahiyar Afirka a kasar Sin, wadda ke da yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4, ba tare da biyan harajin kwastam ko kwabo ba. Hakan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin daidaita yanayin cinikin da take yi tare da kasashen Afirka.
Ban da haka, Mista Tella ya ambaci yadda manufar Sin ta yafe harajin kwastam za ta amfani kasashen Afirka a kokarinsu na raya masana’antu. A cewarsa, tun daga lokacin mulkin mallaka har zuwa yanzu, kasashen Afirka sun dade suna fitar da danyun kayayyaki, da shigar da kayayyakin masana’antu da aka sarrafa daga sauran kasashe, lamarin da ya sa su rashin samun damar adana kudi. Sai dai sabuwar manufar kasar Sin ta yafe harajin kwastam za ta karfafa wa ‘yan kasuwa gwiwa domin a sarrafa danyun kayayyaki a kasashen Afirka kafin a fitar da su, da zummar daga darajar kayayyakin a kasuwannin kasar Sin.
Haka zalika, Babajide Tella ya ce manufar kasar Sin ta amfanar da kasashen Afirka ta sa kaimi ga kasashen yamma domin su daidaita manufofinsu masu alaka da nahiyar Afirka. A cewarsa, kasashen yamma na ganin cewa, matakin kasar Sin na yafe harajin kwastam zai ba kasar damar samar da karin tasiri a nahiyar Afirka. Saboda haka, kasashen yamma suna kokarin daidaita manufofinsu da suka shafi nahiyar Afirka don kara janyo hankulan kasashen Afirka, da zummar takara da kasar Sin.
To, bayan karanta bayanin da Mista Babajide Tella ya rubata, ina so in ce, na yarda da yawancin ra’ayoyinsa. Sai dai na ga kamar bai samu cikakkiyar fahimtar dalilin da ya sa kasar Sin ta kuduri aniyar yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam ba. Sau da dama ya ambaci yadda kasar Sin ke “yin tasiri”, tamkar dai abun da kasar Sin ke nema daya ne da na kasashen yamma. Amma a hakika, ainihin dalilin da ya sa kasar Sin daukar mataki na amfanar da kasashen Afirka shi ne burin kasar na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.
A ganin kasar Sin, mabambantan kasashe da al’ummu suna bukatar kasancewa tare da juna a duniyarmu. Saboda haka, a lokacin da wata kasa ke neman habaka moriyar kanta, ya kamata ta lura da damuwar sauran kasashe, da ba kasashe daban daban damar samun ci gaba na bai daya. Wannan tunani ya sa kasar Sin kullum take neman kulla huldar hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna tare da sauran kasashe, maimakon matakan cin moriya da faduwar wani da wasu kasashen yamma suka saba daukawa.
Wannan tunani ne ma ya sa kasar Sin bude kasuwanninta ga kasashen Afirka, a lokacin da wasu manyan kasashe ke kokarin saka shingayen ciniki. Hakika matakin yafe harajin kwastam da kasar Sin ke dauka a wannan karo ya riga ya zarce tsarin ciniki da na tattalin arziki, inda ya zamanto misalin yadda kasar Sin ke kokarin samar da gudunmowa wajen gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya. (Bello Wang)















Discussion about this post