ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Yafe Harajin Kwastam Ga Afirka: Alfanun Abin Ya Zarce Batun Cinikayya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Daga ranar 1 ga watan Mayun bana, kasar Sin za ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da suke sayarwa a kasuwanninta. Dangane da manufar, Babajide Tella, wani malami na jami’ar Howard ta kasar Amurka ya yi tsokaci, wanda aka wallafa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria a kwanan baya.

A cewar Mista Tella, manufar nan ta kasar Sin, da farko dai, ta ba kasashen Afirka damammakin shigar da kayayyakinsu cikin kasuwannin Sin. Za a iya sayar da amfanin gona da sauran kayayyakin da aka kera a nahiyar Afirka a kasar Sin, wadda ke da yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4, ba tare da biyan harajin kwastam ko kwabo ba. Hakan ya nuna sahihancin kasar Sin a fannin daidaita yanayin cinikin da take yi tare da kasashen Afirka.

Ban da haka, Mista Tella ya ambaci yadda manufar Sin ta yafe harajin kwastam za ta amfani kasashen Afirka a kokarinsu na raya masana’antu. A cewarsa, tun daga lokacin mulkin mallaka har zuwa yanzu, kasashen Afirka sun dade suna fitar da danyun kayayyaki, da shigar da kayayyakin masana’antu da aka sarrafa daga sauran kasashe, lamarin da ya sa su rashin samun damar adana kudi. Sai dai sabuwar manufar kasar Sin ta yafe harajin kwastam za ta karfafa wa ‘yan kasuwa gwiwa domin a sarrafa danyun kayayyaki a kasashen Afirka kafin a fitar da su, da zummar daga darajar kayayyakin a kasuwannin kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Babajide Tella ya ce manufar kasar Sin ta amfanar da kasashen Afirka ta sa kaimi ga kasashen yamma domin su daidaita manufofinsu masu alaka da nahiyar Afirka. A cewarsa, kasashen yamma na ganin cewa, matakin kasar Sin na yafe harajin kwastam zai ba kasar damar samar da karin tasiri a nahiyar Afirka. Saboda haka, kasashen yamma suna kokarin daidaita manufofinsu da suka shafi nahiyar Afirka don kara janyo hankulan kasashen Afirka, da zummar takara da kasar Sin.

To, bayan karanta bayanin da Mista Babajide Tella ya rubata, ina so in ce, na yarda da yawancin ra’ayoyinsa. Sai dai na ga kamar bai samu cikakkiyar fahimtar dalilin da ya sa kasar Sin ta kuduri aniyar yafe wa kasashen Afirka harajin kwastam ba. Sau da dama ya ambaci yadda kasar Sin ke “yin tasiri”, tamkar dai abun da kasar Sin ke nema daya ne da na kasashen yamma. Amma a hakika, ainihin dalilin da ya sa kasar Sin daukar mataki na amfanar da kasashen Afirka shi ne burin kasar na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

A ganin kasar Sin, mabambantan kasashe da al’ummu suna bukatar kasancewa tare da juna a duniyarmu. Saboda haka, a lokacin da wata kasa ke neman habaka moriyar kanta, ya kamata ta lura da damuwar sauran kasashe, da ba kasashe daban daban damar samun ci gaba na bai daya. Wannan tunani ya sa kasar Sin kullum take neman kulla huldar hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna tare da sauran kasashe, maimakon matakan cin moriya da faduwar wani da wasu kasashen yamma suka saba daukawa.

Wannan tunani ne ma ya sa kasar Sin bude kasuwanninta ga kasashen Afirka, a lokacin da wasu manyan kasashe ke kokarin saka shingayen ciniki. Hakika matakin yafe harajin kwastam da kasar Sin ke dauka a wannan karo ya riga ya zarce tsarin ciniki da na tattalin arziki, inda ya zamanto misalin yadda kasar Sin ke kokarin samar da gudunmowa wajen gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.