ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kurakuran Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

by Sulaiman
4 years ago
Tarbiyya

Assalamu Alaikum! Masu karatu barkanmu da sake kasancewa da ku a cikin wannnan shiri, idan ba a manta ba muna bayani ne a kan KURAKURAN IYAYE WAJEN TARBIYYA, inda a makon jiya muka fara tabo batun yadda bai kamata iyaye mata suna bari ana yi wa ‘ya’yansu wasu abubuwa da suka shafi al’aurarsu ba irin su tsarki da wankin ‘inner wares’ wanda ko ga mutane nakusa abin na da illa ballantana na nesa.

A nan zan yi jan hankali gare mu mata mu sani ita ‘ya mace jikinta ba kamar na namiji ba ne, halittarsu ta bambanta wanda bai kamata a ce jinsi daban na taba ta kuma har yana mata tsarki ba, dan za ta iya jin wani yanayi a jikinta da tunanin abin da hankalinsu bai kamata a ce ya kai ba a shekarunsu.

Amma saboda wadannan abubuwan na jikinsu za su iya fara ji. Da wannan nake cewa ya kamata duk abunda ya shafi Mace duk kankantarta a matsayinki na Uwa ki tsaya ki dauke shi ‘serious’ sosai, kar ki ce dan’uwanta ne uwa daya uba daya da sauransu, ba haka abin yake ba.

ADVERTISEMENT

Wadannan abubuwa suna daga matsalolin da muke fuskanta a wadannan lokuta, ya kamata iyaye mu gane mu kara tsayawa wajen kulawa da tarbiyyar yaranmu mata da maza. Idan mace za ta iya jin wani abu a jikinta da kai tunaninta wani wuri daban, ya kuke gani ga da namiji?. Wankin ‘pants’ ko in ce ‘inners’ sai in ga kamar rashin sanin darajar kanki ne kawai zai sa ba za ki wanke ‘inners’ dinki da na yaranki mata ba ko da ‘yar yarinya ce ba, bare harya zamana kina diba ki ba dan malam wankinsu ko yaranki maza. Ki ba da kayan wanki amma ‘inners’ dinki su ne asalin sirrinki, ta yaya za ki ba almajiri wanki ‘inners’ dinki ko na diyanki, dan Allah mata mu gyara wannan, a cire kiwa da ganda.

Lallai akwai lokacin da ya kamata Uba ya ja ‘yarshi Mace a jiki musamman idan ta soma girma a wannan lokutan kar ya ce komai Uwa ce, ita mace ce da sauransu domin yin hakan kamar ya ba wani katone a waje damar bata mishi ‘ya musamman a irin zamanin da muke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

GORON JUMA’A 22-05-2026

Wasu iyaye mazan da yayyu Maza ba su san a wata ya kamata a ce sun cire mata kudi ko sun siyo mata abubuwan bukata musamman ‘Pad’ kunzugu, ‘yan kayan kyalekyali da sauransu har sai ka ga wani kato ya soma jan ra’ayinta da ire-iren wadannan abubuwan yana kashe mata kudi da sauransu.

Tun da a gida mahaifi bai da lokacinta sam bare ya san me take ciki me take bukata, haka yayyunta maza sai barazanar shi yayanta ne amma bai taba sanin tana bukatar ‘Pad’ ko wasu abubuwan bukata ba sam ba ruwansa, wani wayar hannunta ma bai san ina ta samo ba.

Iyaye mata na da rauni kan ire-iren abubuwan nan sosai, to kusan a wannan zamanin akan yi sa’a da iyaye Maza marasa lokacin kulawa sam ba su da lokaci sai an yi laifi su yi ihu su wuce shikenan wanda hakan ba zai hana gobe a kuma ba sam, ALLAH ya sa mudace Amin.

A halin yanzu kuma ga wasu shawarwari gare mu a matsayinmu na iyaye kamar haka:
1. Mu guji aikata munanan abubuwa saboda yaranmu na ganin duk abin da muke ba ma boye musu saboda bacin watarana. In za ka bada tarbiya ka ba da me kyau wanda al’umma za su amfana Manzon Allah (SAW) ya yi alfahari da shi, to mu zama nagari.
2. Iyaye su guji yin wasu abubuwa a gaban ‘ya’yansu kamarsu fada wanda an san yau da gobe da kuma aikata Sunnah yayin da ‘ya’yansu ke guri ko farke. Yana da kyau da yaro ya bude baki inda hali a raba shi da dakin iyayen. Domin fadin Manzon Allah ne (SAW) “Narantse da wanda raina ke hannunsa, da namiji zai sadu da matarsa kuma a cikin dakin akwai yaron da yake farke yana ganinsu yana jin kalamansu, da numfashinsu ba zai rabauta ba har abada, idan yarone zai zama mazinaci, idan yarinya ce ta zama Mazinaciya”. Wannan Hadisi yana nuna illar kwana daki daya da yaro wanda ke da wayau, dan haka shi ma yana daga cikin manyan abubuwan da ke lalata tarbiya, iyaye mukiyaye. A nan za mu dasa Aya Allah ya ba mu ikon gyarawa Amin.

 

Tarbiyya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
Labarai

Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

April 17, 2026
Next Post
Yadda Ake Hada Yeast

Yadda Ake Hada Yeast

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.