Bisa gayyatar da shugaban kasar Djibouti, Ismail Omar Guelleh ya yi, manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, mista Losang Jamcan, ya halarci bikin rantsar da shugaba Guelleh, a birnin Djibouti, jiya Asabar.
Kana duk a jiya, shugaba Guelleh na kasar Djibouti ya gana da Losang Jamcan, wanda shi ma ya kasance mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, a fadar People’s Palace, dake birnin Djibouti.Yayin ganawarsu, Losang Jamcan ya isar da gaisuwa da fatan alheri na shugaba Xi Jinping na Sin, ga shugaba Guelleh.
Kana jami’in ya ce, huldar abota dake tsakanin kasashen biyu, mai shafar manyan tsare-tsare na dukkan fannoni, na dada shiga mataki mai zurfi, karkashin jagorancin shugabannin kasashen Djibouti da Sin.
Kana kasar Sin tana son aiki tare da bangaren Djibouti wajen aiwatar da matsaya daya da shugabannin biyu suka cimma, da habaka hadin gwiwa a kokarin ciyar da huldar dake tsakanin kasashen biyu zuwa gaba.
A nasa bangare, shugaba Guelleh na kasar Djibouti ya bayyana godiyarsa ga takwaransa na Sin Xi Jinping, bisa yadda ya aike da manzonsa na musamman domin halartar bikin rantsar da shi.
Ya kara da cewa, kasar Sin aminiya ce ta kasar Djibouti, da za ta iya dogaro da ita a ko da yaushe. Kana bangaren Djibouti na son karfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin, da kara yin mu’amala kan harkoki daban daban, da kokarin hadin kai da juna yayin da suke kula da al’amuran kasa da kasa. (Bello Wang)















Discussion about this post