ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Yekuwar Daukar Matakin Gaggawa Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu, Sulaiman and Adamu Yusuf Indabo
2 months ago
Jarida

Gidauniyar ci gaban kafofin yada labarai ta Afirka (AMDF) ta yi yekuwar daukar matakin gaggawa kan take ‘yancin jarida, domin ta ce ‘yancin ‘yan jaeida na fuskantar babban barazana a yankin Afirka. 

Gidauniyar ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2026, gidauniyar AMDF ta nuna damuwarta kan ci gaba da tabarbarewar ‘yancin ‘yan jarida a fadin Nahiyar Afirka.

Daga nazarin gidauniyar kan ‘yancin ‘yan jarida, ta bayyana cewa yanayin ‘yancin ‘yan jarida a Afirka na raguwa, inda ‘yan jarida ke fuskantar tashin hankali da danniya da hana gudanar da aiki kan tsari.

ADVERTISEMENT

Kiddigar ‘yancin ‘yan na gidauniyar AMDF a tsakanin 2025 zuwa 2026, sun nuna wasu daga cikin abubuwan da suka fi tayar da hankali. A cewarta, a kasar Sudan ba kawai ta zama mafi yawan kisan ‘yan jarida a Nahiyar ba a 2025 ba, har ma tana da tarihin mafi yawan ‘yan jarida da suka bace. Ta ce wannan abin damuwar na nuna hadarin da masu aikin jarida ke fuskanta, musamman a wuraren da ake rikici da kuma wadanda ke cikin rashin kwanciyar hankali.

Binciken ya gano cewa, kasar Eritrea na ci gaba da zama kasar Afirka da ke tsare ‘yan jarida mafi yawa, inda ta kama ‘yan jarida ba bisa ka’ida ba tare da musguna musu.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Kazalika, kiddigar a fadin yankin Sahel, musamman a Nijar da Mali da Burkina Faso da gwamnatocin sojoji ke jagoranta sun kara tsananta matakan kan ‘yan jarida masu zaman kansu, suna adawa yaduwar bayanai. A yankin manyan tafkuna, ciki har da Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo da Rwanda da Burundi, aikin jarida na kara zama laifi, inda ake tauye ‘yan jarida da cin zarafi da gurfanarwa a kotu da tsoratarwa.

Haka kuma a Yammacin Afirka, Nijeriya ta bambanta a matsayin daya daga cikin mafi hadari ga ‘yan jarida, tare da farmaki akai-akai daga gwamnatoci da masu zaman kansu. Wadannan al’amuran suna nuna wani babban yanayi da ‘yancin aikin jarida ke fuskantar matsin lamba.

Binciken AMDF ya gano kasashe biyar da ake tauye ‘yancin ‘yan jarida sosai, kasashen sun hada da Eritrea, Djibouti, Sudan, Habasha, da Rwanda. A cikin wadannan kasashen, aikin jarida na cikin kuntatawa sosai, kuma ‘yan jarida suna fuskantar hadarin kama su ba bisa ka’ida ba, ana azabtar da su wani lokaci ma har a kashe su.

“Shaidu daga nau’o’i daban-daban na bin diddigi, ciki har da namu, suna nuni da sakamakon guda daya, ‘yancin ‘yan jarida a Afirka yana karkashin barazana mai tsanani,” in ji AMDF.

AMDF ta kira ga gwamnatocin Afirka su kiyaye alkawuran kundin tsarin mulki da ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin ‘yan jarida.

Jarida
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Jarida
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Jarida
Adamu Yusuf Indabo
+ posts Bio
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Da Akwai Hikima, Na Yanzu Sai Karyar Zuwa Waje – Amina
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Ba Nanaye Ko Rashin Da’a Nake Rubutawa Ba – A.S Aikawa
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubuta Tamkar Madubi Suke Ga Al’ummah – Zainab Salihu Yarima

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da 'Ya'yansu Alkur'ani (2)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.