Gidauniyar ci gaban kafofin yada labarai ta Afirka (AMDF) ta yi yekuwar daukar matakin gaggawa kan take ‘yancin jarida, domin ta ce ‘yancin ‘yan jaeida na fuskantar babban barazana a yankin Afirka.
Gidauniyar ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2026, gidauniyar AMDF ta nuna damuwarta kan ci gaba da tabarbarewar ‘yancin ‘yan jarida a fadin Nahiyar Afirka.
Daga nazarin gidauniyar kan ‘yancin ‘yan jarida, ta bayyana cewa yanayin ‘yancin ‘yan jarida a Afirka na raguwa, inda ‘yan jarida ke fuskantar tashin hankali da danniya da hana gudanar da aiki kan tsari.
Kiddigar ‘yancin ‘yan na gidauniyar AMDF a tsakanin 2025 zuwa 2026, sun nuna wasu daga cikin abubuwan da suka fi tayar da hankali. A cewarta, a kasar Sudan ba kawai ta zama mafi yawan kisan ‘yan jarida a Nahiyar ba a 2025 ba, har ma tana da tarihin mafi yawan ‘yan jarida da suka bace. Ta ce wannan abin damuwar na nuna hadarin da masu aikin jarida ke fuskanta, musamman a wuraren da ake rikici da kuma wadanda ke cikin rashin kwanciyar hankali.
Binciken ya gano cewa, kasar Eritrea na ci gaba da zama kasar Afirka da ke tsare ‘yan jarida mafi yawa, inda ta kama ‘yan jarida ba bisa ka’ida ba tare da musguna musu.
Kazalika, kiddigar a fadin yankin Sahel, musamman a Nijar da Mali da Burkina Faso da gwamnatocin sojoji ke jagoranta sun kara tsananta matakan kan ‘yan jarida masu zaman kansu, suna adawa yaduwar bayanai. A yankin manyan tafkuna, ciki har da Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo da Rwanda da Burundi, aikin jarida na kara zama laifi, inda ake tauye ‘yan jarida da cin zarafi da gurfanarwa a kotu da tsoratarwa.
Haka kuma a Yammacin Afirka, Nijeriya ta bambanta a matsayin daya daga cikin mafi hadari ga ‘yan jarida, tare da farmaki akai-akai daga gwamnatoci da masu zaman kansu. Wadannan al’amuran suna nuna wani babban yanayi da ‘yancin aikin jarida ke fuskantar matsin lamba.
Binciken AMDF ya gano kasashe biyar da ake tauye ‘yancin ‘yan jarida sosai, kasashen sun hada da Eritrea, Djibouti, Sudan, Habasha, da Rwanda. A cikin wadannan kasashen, aikin jarida na cikin kuntatawa sosai, kuma ‘yan jarida suna fuskantar hadarin kama su ba bisa ka’ida ba, ana azabtar da su wani lokaci ma har a kashe su.
“Shaidu daga nau’o’i daban-daban na bin diddigi, ciki har da namu, suna nuni da sakamakon guda daya, ‘yancin ‘yan jarida a Afirka yana karkashin barazana mai tsanani,” in ji AMDF.
AMDF ta kira ga gwamnatocin Afirka su kiyaye alkawuran kundin tsarin mulki da ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin ‘yan jarida.















Discussion about this post