ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Yekuwar Daukar Matakin Gaggawa Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu, Sulaiman and Adamu Yusuf Indabo
4 weeks ago
Jarida

Gidauniyar ci gaban kafofin yada labarai ta Afirka (AMDF) ta yi yekuwar daukar matakin gaggawa kan take ‘yancin jarida, domin ta ce ‘yancin ‘yan jaeida na fuskantar babban barazana a yankin Afirka. 

Gidauniyar ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2026, gidauniyar AMDF ta nuna damuwarta kan ci gaba da tabarbarewar ‘yancin ‘yan jarida a fadin Nahiyar Afirka.

Daga nazarin gidauniyar kan ‘yancin ‘yan jarida, ta bayyana cewa yanayin ‘yancin ‘yan jarida a Afirka na raguwa, inda ‘yan jarida ke fuskantar tashin hankali da danniya da hana gudanar da aiki kan tsari.

ADVERTISEMENT

Kiddigar ‘yancin ‘yan na gidauniyar AMDF a tsakanin 2025 zuwa 2026, sun nuna wasu daga cikin abubuwan da suka fi tayar da hankali. A cewarta, a kasar Sudan ba kawai ta zama mafi yawan kisan ‘yan jarida a Nahiyar ba a 2025 ba, har ma tana da tarihin mafi yawan ‘yan jarida da suka bace. Ta ce wannan abin damuwar na nuna hadarin da masu aikin jarida ke fuskanta, musamman a wuraren da ake rikici da kuma wadanda ke cikin rashin kwanciyar hankali.

Binciken ya gano cewa, kasar Eritrea na ci gaba da zama kasar Afirka da ke tsare ‘yan jarida mafi yawa, inda ta kama ‘yan jarida ba bisa ka’ida ba tare da musguna musu.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Kazalika, kiddigar a fadin yankin Sahel, musamman a Nijar da Mali da Burkina Faso da gwamnatocin sojoji ke jagoranta sun kara tsananta matakan kan ‘yan jarida masu zaman kansu, suna adawa yaduwar bayanai. A yankin manyan tafkuna, ciki har da Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo da Rwanda da Burundi, aikin jarida na kara zama laifi, inda ake tauye ‘yan jarida da cin zarafi da gurfanarwa a kotu da tsoratarwa.

Haka kuma a Yammacin Afirka, Nijeriya ta bambanta a matsayin daya daga cikin mafi hadari ga ‘yan jarida, tare da farmaki akai-akai daga gwamnatoci da masu zaman kansu. Wadannan al’amuran suna nuna wani babban yanayi da ‘yancin aikin jarida ke fuskantar matsin lamba.

Binciken AMDF ya gano kasashe biyar da ake tauye ‘yancin ‘yan jarida sosai, kasashen sun hada da Eritrea, Djibouti, Sudan, Habasha, da Rwanda. A cikin wadannan kasashen, aikin jarida na cikin kuntatawa sosai, kuma ‘yan jarida suna fuskantar hadarin kama su ba bisa ka’ida ba, ana azabtar da su wani lokaci ma har a kashe su.

“Shaidu daga nau’o’i daban-daban na bin diddigi, ciki har da namu, suna nuni da sakamakon guda daya, ‘yancin ‘yan jarida a Afirka yana karkashin barazana mai tsanani,” in ji AMDF.

AMDF ta kira ga gwamnatocin Afirka su kiyaye alkawuran kundin tsarin mulki da ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin ‘yan jarida.

Jarida
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
Jarida
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Jarida
Adamu Yusuf Indabo
+ posts Bio
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Da Akwai Hikima, Na Yanzu Sai Karyar Zuwa Waje – Amina
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Ba Nanaye Ko Rashin Da’a Nake Rubutawa Ba – A.S Aikawa
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubuta Tamkar Madubi Suke Ga Al’ummah – Zainab Salihu Yarima

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da 'Ya'yansu Alkur'ani (2)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.