ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Yekuwar Daukar Matakin Gaggawa Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu, Sulaiman and Adamu Yusuf Indabo
2 months ago
Jarida

Gidauniyar ci gaban kafofin yada labarai ta Afirka (AMDF) ta yi yekuwar daukar matakin gaggawa kan take ‘yancin jarida, domin ta ce ‘yancin ‘yan jaeida na fuskantar babban barazana a yankin Afirka. 

Gidauniyar ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2026, gidauniyar AMDF ta nuna damuwarta kan ci gaba da tabarbarewar ‘yancin ‘yan jarida a fadin Nahiyar Afirka.

Daga nazarin gidauniyar kan ‘yancin ‘yan jarida, ta bayyana cewa yanayin ‘yancin ‘yan jarida a Afirka na raguwa, inda ‘yan jarida ke fuskantar tashin hankali da danniya da hana gudanar da aiki kan tsari.

ADVERTISEMENT

Kiddigar ‘yancin ‘yan na gidauniyar AMDF a tsakanin 2025 zuwa 2026, sun nuna wasu daga cikin abubuwan da suka fi tayar da hankali. A cewarta, a kasar Sudan ba kawai ta zama mafi yawan kisan ‘yan jarida a Nahiyar ba a 2025 ba, har ma tana da tarihin mafi yawan ‘yan jarida da suka bace. Ta ce wannan abin damuwar na nuna hadarin da masu aikin jarida ke fuskanta, musamman a wuraren da ake rikici da kuma wadanda ke cikin rashin kwanciyar hankali.

Binciken ya gano cewa, kasar Eritrea na ci gaba da zama kasar Afirka da ke tsare ‘yan jarida mafi yawa, inda ta kama ‘yan jarida ba bisa ka’ida ba tare da musguna musu.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Kazalika, kiddigar a fadin yankin Sahel, musamman a Nijar da Mali da Burkina Faso da gwamnatocin sojoji ke jagoranta sun kara tsananta matakan kan ‘yan jarida masu zaman kansu, suna adawa yaduwar bayanai. A yankin manyan tafkuna, ciki har da Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo da Rwanda da Burundi, aikin jarida na kara zama laifi, inda ake tauye ‘yan jarida da cin zarafi da gurfanarwa a kotu da tsoratarwa.

Haka kuma a Yammacin Afirka, Nijeriya ta bambanta a matsayin daya daga cikin mafi hadari ga ‘yan jarida, tare da farmaki akai-akai daga gwamnatoci da masu zaman kansu. Wadannan al’amuran suna nuna wani babban yanayi da ‘yancin aikin jarida ke fuskantar matsin lamba.

Binciken AMDF ya gano kasashe biyar da ake tauye ‘yancin ‘yan jarida sosai, kasashen sun hada da Eritrea, Djibouti, Sudan, Habasha, da Rwanda. A cikin wadannan kasashen, aikin jarida na cikin kuntatawa sosai, kuma ‘yan jarida suna fuskantar hadarin kama su ba bisa ka’ida ba, ana azabtar da su wani lokaci ma har a kashe su.

“Shaidu daga nau’o’i daban-daban na bin diddigi, ciki har da namu, suna nuni da sakamakon guda daya, ‘yancin ‘yan jarida a Afirka yana karkashin barazana mai tsanani,” in ji AMDF.

AMDF ta kira ga gwamnatocin Afirka su kiyaye alkawuran kundin tsarin mulki da ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin ‘yan jarida.

Jarida
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Jarida
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai
  • Sulaiman
    Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
Jarida
Adamu Yusuf Indabo
+ posts Bio
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Da Akwai Hikima, Na Yanzu Sai Karyar Zuwa Waje – Amina
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Ba Nanaye Ko Rashin Da’a Nake Rubutawa Ba – A.S Aikawa
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubuta Tamkar Madubi Suke Ga Al’ummah – Zainab Salihu Yarima

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Next Post
Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da 'Ya'yansu Alkur'ani (2)

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.