ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Gwamnan Kano Bai Halarci Sauya Sheƙar Abba Zuwa APC Ba

by Sadiq
6 months ago
Kano

Mataimakin gwamnan Jihar Kano, Comrade Abdulsalam Gwarzo, bai halarci taron sauya sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jami’yyar APC ba, abin da ke nuna yiwuwar rashin jituwa a tsakaninsu.

Gwamna Abba, ya ce koma APC ne domin yin aiki tare da gwamnatin tarayya da kuma kawo kwanciyar hankali, ci gaba, da bunƙasa a Kano.

  • Da Gaske Ne Wasu Jami’ai 16 Sun Yi Yunƙurin Kifar Da Gwamnatin Tinubu — DHQ
  • Mataimakin Gwamna Yusuf Bai Halarci Taron Sauya Sheƙar Maigidansa Zuwa APC Ba

Ya jaddada cewa wannan mataki ba na ƙashin kansa ba ne, kuma ya tabbatar da cewa biyayya da kishin Jihar Kano sun fi komai muhimmanci a wajensa.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana cewa shawarar komawa jam’iyyar ta biyo bayan tattaunawa da majalisar gwamnatinsa, shugabannin ƙananan hukumomi, ‘yan majalisa, da sauran masu ruwa da tsaki a siyasa.

Ya ce komawa jam’iyyar da ke mulki a matakin tarayya zai samar da ayyukan ci gaba da inganta yi wa al’umma hidima.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Haka kuma, Gwamnan ya sanar da shirin kafa Kwamitin Manyan Mutane a Kano, wanda zai zama majalisar shawara kan ci gaba da warware rikice-rikice, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta kasance mai haɗa kan kowa da kowa.

Ya kuma yi kira ga al’umma su yi rajista da jam’iyyar APC domin tunkarar zaɓen 2027.

Taron ya samu halartar manyan jami’an APC ciki har da tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, da sauran shugabanni. Shugaban APC na Kano, ciki har da Abdullahi Abbas.

Masu sharhi kan al’amuran siyasa sun ce wannan mataki na iya sauya tsarin siyasa a Kano kafin zaɓen 2027.

Da yawa suna ganin rashin halartar mataimakin gwamnan na nuna irin rashin jituwar da ke tsakaninsu wanda hakan zai iya shafar harkokin siyasa a jihar.

MASU ALAKA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Next Post
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Dalilan Da Suka Sa Na Sauya Sheƙa Zuwa Jami'yyar APC - Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.