sssalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
A wannan lokaci kuma a wannan gaba, kamar kowane mako zan yi magana kan wasu abubuwa, wadanda suke faruwa a wannan kasa ta Nijeriya, musamman arewacin Nijeriya.
Mu ne talauci, rashin ilimi, matsaloli rashin sana’a, fadace-fadacen daba, fadan siyasa, matsaloli tsakanin shugabanni, da sauransu. Mu suka fi addaba, kuma alal hakikanin gaskiya akwai abubuwa da yawa da ya kamata mu tsaya mu yi karatun ta nutsu, mu san ya za a yi mu kiyaye gaba.
Abubuwan sun fara faruwa yanzu tun asali ba a magance ba, wanda a lokacin ‘da’ za a ga makoci in zai saka dan shi a makaranta ya kan saka dukka yaran makotansa ko na layin ma in da hali.
Ko kuma ka ga uba ya je ya saka ‘ya’yan wansa a makaranta da sauransu, irin wannan abubuwan. Ko ka ga mai kudi ma ya dauki nauyin iyalan wadanda suka rasu ya saka su a makaranta, saboda dai kar yaran su zauna.
Kuma babban abin bakin cikin yanzu shi ne, za a ga yaro dan (3-4-5yrs) akan titi yana bara ko yana tallah. Ko ka ga yarinya mace ‘yar karama wacce ya kamata ace tana makarantar islamiyya ko na boko sai ka ganta tana yin Awara ko wainar fulawa irin wannan ‘something like this’.
Lokacin kuma da ya kamata a ce yarinyar ta tsaya ta amfani wannan, sai ka ga dabi’un namu, me ya sa al’ummar ta zama haka?. Daga magidanci ya mutu ya bar yara uku-hudu, sai ka ga kawai ba sa samun tallafi, ba sa samun taimako. Sai ka ga Uwar idan bata dora yaran irin wannan tallukan sun dan yi awara, dan kosai ko wani abu wanda za su yi sutturar sallah, su ci abinci ba da sauransu.
Irin wadannan dabi’u gaskiya sun ba da gudummawa gurin lalata yara ‘ya’ya mata, da su kansu mazan ma gurin ko shaye-shaye. Yaro ya saba cin abinci ko yunwa ta ishe shi/ishe ta. Toh, dole idan suka rasa sai sun bi wannan hanyoyin da zasu ci abinci.
Ya kamata mu yi karatun ta nutsu, kullum zagin shugabanni muke, idan ma da laifin shugabanni da laifinmu, ya za a yi mu gyara irin wadannan matsalolin, mun sauka daga kan kadamin da addini ya sa mu bi, idan kana da dama ka taimaki na kasa da kai, ka taimaki makofcinka, da an saukar da wanda zai ci gadonka ban da iyalanka da makofcinka zai ci.
Addini ya nuna mana duk irin wadannan abubuwan duk mun watsar, yanzu daga kai sai ‘ya’yanka, za ka ga idan sallah ce. Idan aka samu ‘control’ kamar yadda yake a da, za ka ga mutum unguwar ma gaba daya zai fada a ji saboda ya taimaka.
Ina ganin al’umma mu yi addu’a, mu dawo jan wannan gabar, wallahi sai Allah ya taimake mu. Dan Allah da Annabi a taimaka.
Wassalamu alaikum.















Discussion about this post