Asslamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkan mu da kasancewa a wannan rana ta juma’a, Allah ya ba mu ladan dake cikinta amin.
A wannan bigire zan yi maganganu guda biyu zuwa uku na jan hankali, wanda ya kamata ace dukkanin ƴan’uwa musulmi musamman waɗanda suke wannan ƙasa ta mu ta najeriya suke kuma Jihar Kano ko na ce Arewacin Najeriya, kuma kusan na ce musulmai, dan abun ya fi shafar su.
Addu’a: Dole mu yi addu’a dangane da wasu masifu da suke faruwa na kwacen waya, saboda wannan ba ƙaramin masifa ba ce, kamar yaƙi ne babbar musiba ce wannan abun na kwacen waya ana ganin shi a hankali-a hankali to, nema yake fa ya fi ƙarfin gwamnati.
Domin ita gwamnati ta kasa magance matsalar kwacen wayar domin tun ana soke-soken wuƙa da sare-sare yanzu ya koma rasa rayuka ake yi kai tsaye, ba babba ba yaro ba talaka ba mai kuɗi ba me mulki ba me sarauta, sannan ba me muƙami. Kowa ya kan iya rasa ransa to, me ya kamata mu yi?
Ya kamata malaman mu su yi amfani da wannan dama a masallatai a yi ta addu’a “ubangiji wannan musifa da ka jarabce mu da ita Allah ubangiji ka yaye mana ita ka ba mu ikon cinye ta.
Tabbas wannan abu ne daya kamata mu maida hankali a kai, masu gidaje masu ‘ya’ya ku tsaya ku ja wa ‘yaƴanku kunnuwa yawan shiga inda bai kamata ba, yawan shiga taruka shi ma matsala ne, wani ya kan iya shafa. Yayin da gwamnati ta hankalta ko abu yayi mata yawa to fa za ta yi kan me uwa dawabi.
Iyaye su riƙa ja wa ‘yaƴansu kunne idan ka ga ɗanka da wayar da ba ta kamata ba, ko ba tashi ba, ko ba kai ka siya masa ba, kuma bai da kuɗin da zai mallaki wannan wayar, ya kamata ka tsawatar masa daga ina ya samo ta?, domin a magance tun daga tushe.
Idan saurayi ne ya kawo wa ‘yarka waya ko ‘yarki waya ku bunciki ta’ina ma wayar ta fito?, a ina ya same ta? mene sana’arsa? .
Magana ta gaskiya abu ne babba wanda idan aka jawo hankali a kai to, da yawa za a ji kunya. Mu yi addu’a sosai addu’a maganin komai ce domin takobin mumini ce, wannan abun na satar waya wallahi masifa ne wallahi sai mun yi addu’o’i da yawa sai mun nemi mafuta a gurin ubangiji tabbas Allah baya aiko wa Al’umma abu kurum, sai idan akwai wani lefi da suka yi gare shi to, mu yi ta tuba mu yi addu’a.
Malamai su yi amfani da wannan dama, ƴan siyasar mu su rufe kunne su rufe idon su, su mai da kai ɗaya, domin mafi yawanci masu waɗannan abubuwan yaransu ne, shi ya sa ko da an kama yaro za ka ga yaro baya daɗewa za ka ga ya fito.
Ya kamata a zauna da su indai al’umma ne a gabansu a magance wannan matsala, a ɗauki babban mataki a kan wannan matsaloli da suke faruwa na satar waya, ace komai daga cikin arewacin najeriya yake faruwa kuma daga cikin musulmai mu da aka san mu da kiyayewa a cikin addinin mu da komai to, ubangiji Allah ya kawo mana sauƙi Allah ya kawo mana mafita.















Discussion about this post