ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?

by Ibrahim Bala
4 weeks ago
waya

Asslamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkan mu da kasancewa a wannan rana ta juma’a, Allah ya ba mu ladan dake cikinta amin.

A wannan bigire zan yi maganganu guda biyu zuwa uku na jan hankali, wanda ya kamata ace dukkanin ƴan’uwa musulmi musamman waɗanda suke wannan ƙasa ta mu ta najeriya suke kuma Jihar Kano ko na ce Arewacin Najeriya, kuma kusan na ce musulmai, dan abun ya fi shafar su.

Addu’a: Dole mu yi addu’a dangane da wasu masifu da suke faruwa na kwacen waya, saboda wannan ba ƙaramin masifa ba ce, kamar yaƙi ne babbar musiba ce wannan abun na kwacen waya ana ganin shi a hankali-a hankali to, nema yake fa ya fi ƙarfin gwamnati.

ADVERTISEMENT

Domin ita gwamnati ta kasa magance matsalar kwacen wayar domin tun ana soke-soken wuƙa da sare-sare yanzu ya koma  rasa rayuka ake yi kai tsaye, ba babba ba yaro ba talaka ba mai kuɗi ba me mulki ba me sarauta, sannan ba me muƙami. Kowa ya kan iya rasa ransa to, me ya kamata mu yi?

Ya kamata malaman mu su yi amfani da wannan dama a masallatai a yi ta addu’a “ubangiji wannan musifa da ka jarabce mu da ita Allah ubangiji ka yaye mana ita ka ba mu ikon cinye ta.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Tabbas wannan abu ne daya kamata mu maida hankali a kai, masu gidaje masu ‘ya’ya ku tsaya ku ja wa ‘yaƴanku kunnuwa yawan shiga inda bai kamata ba, yawan shiga taruka shi ma matsala ne, wani ya kan iya shafa. Yayin da gwamnati ta hankalta ko abu yayi mata yawa to fa za ta yi kan me uwa dawabi.

Iyaye su riƙa ja wa ‘yaƴansu kunne idan ka ga ɗanka da wayar da ba ta kamata ba, ko ba tashi ba, ko ba kai ka siya masa ba, kuma bai da kuɗin da zai mallaki wannan wayar, ya kamata ka tsawatar masa daga ina ya samo ta?, domin a magance tun daga tushe.

Idan saurayi ne ya kawo wa ‘yarka waya ko ‘yarki waya ku bunciki ta’ina ma wayar ta fito?, a ina ya same ta? mene sana’arsa? .

Magana ta gaskiya abu ne babba wanda idan aka jawo hankali a kai to, da yawa za a ji kunya. Mu yi addu’a sosai addu’a maganin komai ce domin takobin mumini ce, wannan abun na satar waya wallahi masifa ne wallahi sai mun yi addu’o’i da yawa sai mun nemi mafuta a gurin ubangiji tabbas Allah baya aiko wa Al’umma abu kurum, sai idan akwai wani lefi da suka yi gare shi to, mu yi ta tuba mu yi addu’a.

Malamai su yi amfani da wannan dama, ƴan siyasar mu su rufe kunne su rufe idon su, su mai da kai ɗaya, domin mafi yawanci masu waɗannan abubuwan yaransu ne, shi ya sa ko da an kama yaro za ka ga yaro baya daɗewa za ka ga ya fito.

Ya kamata a zauna da su indai al’umma ne a gabansu a magance wannan matsala, a ɗauki babban mataki a kan wannan matsaloli da suke faruwa na satar waya, ace komai daga cikin arewacin najeriya yake faruwa kuma daga cikin musulmai mu da aka san mu da kiyayewa a cikin addinin mu da komai to, ubangiji Allah ya kawo mana sauƙi Allah ya kawo mana mafita.

waya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Bunkasar Sashen Masana’antu Masu Nasaba Da Ayyukan Soji Na Kasar Japan Na Haifar Da Damuwa Daga Sassa Daban Daban

Bunkasar Sashen Masana’antu Masu Nasaba Da Ayyukan Soji Na Kasar Japan Na Haifar Da Damuwa Daga Sassa Daban Daban

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.