ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?

by Ibrahim Bala
5 days ago
waya

Asslamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkan mu da kasancewa a wannan rana ta juma’a, Allah ya ba mu ladan dake cikinta amin.

A wannan bigire zan yi maganganu guda biyu zuwa uku na jan hankali, wanda ya kamata ace dukkanin ƴan’uwa musulmi musamman waɗanda suke wannan ƙasa ta mu ta najeriya suke kuma Jihar Kano ko na ce Arewacin Najeriya, kuma kusan na ce musulmai, dan abun ya fi shafar su.

Addu’a: Dole mu yi addu’a dangane da wasu masifu da suke faruwa na kwacen waya, saboda wannan ba ƙaramin masifa ba ce, kamar yaƙi ne babbar musiba ce wannan abun na kwacen waya ana ganin shi a hankali-a hankali to, nema yake fa ya fi ƙarfin gwamnati.

ADVERTISEMENT

Domin ita gwamnati ta kasa magance matsalar kwacen wayar domin tun ana soke-soken wuƙa da sare-sare yanzu ya koma  rasa rayuka ake yi kai tsaye, ba babba ba yaro ba talaka ba mai kuɗi ba me mulki ba me sarauta, sannan ba me muƙami. Kowa ya kan iya rasa ransa to, me ya kamata mu yi?

Ya kamata malaman mu su yi amfani da wannan dama a masallatai a yi ta addu’a “ubangiji wannan musifa da ka jarabce mu da ita Allah ubangiji ka yaye mana ita ka ba mu ikon cinye ta.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Tabbas wannan abu ne daya kamata mu maida hankali a kai, masu gidaje masu ‘ya’ya ku tsaya ku ja wa ‘yaƴanku kunnuwa yawan shiga inda bai kamata ba, yawan shiga taruka shi ma matsala ne, wani ya kan iya shafa. Yayin da gwamnati ta hankalta ko abu yayi mata yawa to fa za ta yi kan me uwa dawabi.

Iyaye su riƙa ja wa ‘yaƴansu kunne idan ka ga ɗanka da wayar da ba ta kamata ba, ko ba tashi ba, ko ba kai ka siya masa ba, kuma bai da kuɗin da zai mallaki wannan wayar, ya kamata ka tsawatar masa daga ina ya samo ta?, domin a magance tun daga tushe.

Idan saurayi ne ya kawo wa ‘yarka waya ko ‘yarki waya ku bunciki ta’ina ma wayar ta fito?, a ina ya same ta? mene sana’arsa? .

Magana ta gaskiya abu ne babba wanda idan aka jawo hankali a kai to, da yawa za a ji kunya. Mu yi addu’a sosai addu’a maganin komai ce domin takobin mumini ce, wannan abun na satar waya wallahi masifa ne wallahi sai mun yi addu’o’i da yawa sai mun nemi mafuta a gurin ubangiji tabbas Allah baya aiko wa Al’umma abu kurum, sai idan akwai wani lefi da suka yi gare shi to, mu yi ta tuba mu yi addu’a.

Malamai su yi amfani da wannan dama, ƴan siyasar mu su rufe kunne su rufe idon su, su mai da kai ɗaya, domin mafi yawanci masu waɗannan abubuwan yaransu ne, shi ya sa ko da an kama yaro za ka ga yaro baya daɗewa za ka ga ya fito.

Ya kamata a zauna da su indai al’umma ne a gabansu a magance wannan matsala, a ɗauki babban mataki a kan wannan matsaloli da suke faruwa na satar waya, ace komai daga cikin arewacin najeriya yake faruwa kuma daga cikin musulmai mu da aka san mu da kiyayewa a cikin addinin mu da komai to, ubangiji Allah ya kawo mana sauƙi Allah ya kawo mana mafita.

waya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Buƙatar Taimaka Wa Al’umma Ba Sai Sun Yi Roƙo Ba

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Bunkasar Sashen Masana’antu Masu Nasaba Da Ayyukan Soji Na Kasar Japan Na Haifar Da Damuwa Daga Sassa Daban Daban

Bunkasar Sashen Masana’antu Masu Nasaba Da Ayyukan Soji Na Kasar Japan Na Haifar Da Damuwa Daga Sassa Daban Daban

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.