Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkanmu da wannan lokaci, barkanmu da sake kasancewa a wannan fili mai albarka. A wannan mako zan yi magana a kan falalar goman ƙarshe na Zulhajji.
Hadisi ne daga Ibn Abbas (RA) ya ce, “Annabi (s.a.w) ya ce, ranar ɗaya ga watan Zulhajji ita ce rana da Allah (SWT) ya gafartawa Annabi Adam (AS). Wanda ya azumci wannan rana Allah (SWT) zai gafarta masa kowane irin zunubi ne tsakaninsa da shi, domin Allah shi ne me yafe zunubi ba kowa ba.
Rana ta biyu ga Zulhajji ita ce ranar da Allah (SWT) ya karɓi addu’ar Yunusa (AS) ya fitar da shi daga cikin kifin da ya haɗiye shi. Wanda ya azumci wannan ranar yana da lada kwatankwacin wanda ya raya shekara da ibada. Haƙiƙa Allah (SWT) yanata kaho mana ranaku da lokuta da za mu yi abubuwa da zai kankare zunuban da muke yawan aikatawa.
Rana ta uku malamai suka ce ga Zulhajji, rana ce da Allah (SWT) ya karɓi addu’ar Annabi Zakariyya (AS) ya bashi haihuwa, duk wanda ya azumci wannan rana Allah ubangiji (SWT) zai karɓi addu’o’insa.
Rana ta huɗu ga Zulhajji ita ce, ranar da aka haifi Annabi Isah (AS), duk wanda ya azumci wannan rana Allah zai kare shi daga talauci da kuma musiba. Wannan musubu da suke yawan faruwa ka rasa ta kai ta ƙafa, ta ko’ina to, ire-iren waɗannan abubuwa sai ka ga Allah ya tsallakar da kai ko da musulmi za ta shafarwa.
Rana ta biyar ga Zulhajji ita ce ranar da aka haifi Annabi Musa (AS), duk wanda ya azumci wannan rana Allah (SWT) zai kare shi daga munafurci ko azabar kabari.
Rana ta shida ga Zulhajji ita ce ranar da Allah (SWT) ya yi buɗin alkhairi ga Annabi (SAW) fiyayyen halitta, wanda ya azumci wannan rana Allah zai dube shi da rahma kuma ba zai azabtar da shi ba. Allah gafurul rahim.
Rana ta bakwai ga Zulhajji ita ce ranar da Allah (SWT) zai sa a rufe ƙofofin wuta ba za a buɗe su ba, har sai waɗannan kwanaki goma sun wuce. Duk wanda ya azumci wannan rana Allah zai rufe masa ƙofofi talati na tsananin ratuwarsa, ya buɗe masa ƙofofi talatin na sauƙi. Kai! Allah ya sa mu dace.
Rana ta takwas ga Zulhajji ita ce, ranar da Allah (SWT), ranar da ake cewa ranar tarayya. Duk wanda ya azumci wannan rana babu wanda ya san adadinsa sai Allah.
Rana ta tara kuma ga Zulhajji ita ce, ranar hawan arfa, Allah yana gafartawa dukkan alhazan dake gurin arfa, wanda kuma ba ya gurin aikin idan ya azumci wannan rana Allah yana gafarta masa zunubansa na shekarar da ta gabata da kuma shekrar da take tafe.
Ranar goma ga wata kuma ita ce, ranar layya, ga wanda Allah ya horewa abin da zai yi layya, idan ya yanka dabbarsa ɗigon jini na farko da zai fara ɗiga a ƙasa zai zama gafara gare shi da iyalansa. An so wanda zai yi layya da wanda ba zai yi ba ya kama bakinsa har sai bayan an dawo daga sallar idi ya ci abinci ko wani abu daga cikin layyarsa, Allah zai bashi lada wacce ta fi dutsen Uhud girma da nauyi. Kuma ana so ya raba namansa kashi uku. Kashi na farko sadaka, kashi na biyu kyauta, kashi na uku kuma domin iyalai.
Allah ya bamu ikon azumtar wannan ranaku, ya kuma bamu ikon samun wannan falala. Al’umma muna fatan za a riƙa amfani da wannan tunatarwa domin an riga an san tunasarwa ce. Allah ubangiji ya bamu wannan lada, Allah ya sada mu da alkhairan dake ciki, Allah ka haɗa kanmu, Allah shugabanni Allah ka shirye su, wanda ba za su shiryu ba Allah ka canza mana su ka bamu waɗanda suka fi alkhairi. Allah shugabanni duk wanda muke so, da wanda ba ma so indai alkhairi ne Allah ka tabbatar mana da shi ka zaɓa mana shi, domin Allah ka fi mu sanin daidai, ka fi mu sanin wanda ya dace da mu.















Discussion about this post