Makusanci kuma tsohon darektan yada labarai na gwamnatin Kano, Farfesa Sule Yau Sule ya bayyana cewa rigingimu da shar’o’i da suka ki ci suka ki cin yewa a jami’iyar PDP tasa har aka yi zabe a jihohi biyu, Osun da Ogun babu Alamar jam’iyyar PDP a takardar kada kuri’ar, wanda tasa Sardaunan Kano, Malam Ibrahim shekarau ya zauna da makusantansa da masoyansa har da majalisar shura karkashin jagorancin Dakta Umar Mustapha suka amince Sardauna ya nemo wa mabiyansa mafita.
Farfesa Sule wanda kuma shi ne mai magana da yawun Sardauna Kano ya bayyana haka ne a lokacin taron gangamin barin jam’iyyar PDP da kuma komawa APC wanda aka gudanar a fadar Mundubawa da ke Kano a ranar Lahadi da ta gabata.
A cewar Farfesa Sule, kullom siyasar Sardauna sama wa mabiyansa da al’uma mafita yake yi bayan tattaunawa da kuma kawo masala domin a tsira tare a matakin Jihar Kano da Nijeriya baki daya.
Tun da farko a jawabinsa, Malam Shekarau ya bayyana cewa kullum idan matsala ta ki ci ta ki cinyewa, to addanin Musulinci ya ce a tsaya a kalli lamarin domin warware matsala da ta fuskanci jama’a ta hanyar shawarwari da tattaunawa bisa koyarwar addini, wannan ce tasa suka kalli dukkanin jam’iyyun Nijeriya suka ga kowacce da matsala amma dai wace ce tafi sauki, ita ce jamiyyar APC, don haka ska amince wa abokan tafiya a tsohuwar jam’iyyar PDP suka koma APC, a yanzu kuma akwai bukatar kowa ya je ya yanki katin jam’iyyar APC.
Taron dai ya samu halartar jiga-jigan tsofaffin ‘ya’yan jam’iyyar PDP da suka hada da Sanata Bello Hayatu Gwarzo, Alh Aminu Daniya, Alh Yahaya Bagobiri, wanda ake yi wa lakabi da Banjamin Nattanyahu, sai Aminu gurgo Maifilo da sauran magoya bayan Sardaunan Kano.















Discussion about this post