Tsohon ma’ajin jam’iyyar APC na ƙasa, Hon. Alhaji Bala Muhammad Gwagwarwa ya bayyana cewa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ƙirƙiri shirin samar da manufar Kano ce ta farko domi sanya wa Kanawa kishin jiharsu ne.
A cewarsa, an samar da shirin ne domin Jihar Kano ta samu ci gaba da ɓata samu ba a baya, sakamakon raba kan jama’a da yadda wasu suke fifita ra’ayinsu a kan Kano, wanda wannan ya sa Gwamna Abba ba tsayu kan manufarsa ta haɗa kan Kanawa domin kowa ya ba da gudummawarsa ta kowana fanni da ya ƙore kamar ilimi, lafiya, noma, kasuwanci da sauransu.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Alhaji Gwagwarwa ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai.
Har ila yau, ya ƙara da cewa Gwamna Abba ya fifita Kano fiye da ra’ayinsa ba kamar yadda wasu magabata suka yi a lokacin mulkinsu ba, wanda shi ya haifar da matsalar wajen ci gaban Kano.
Haka kuma ya ce wannan manufa ce ta sa Gwamna Abba yake aiki wajen gyara tarbiyya da tunanin matasa na kowa ya dogara da kansa ta hanyar bunƙasa sana’o’in dogaro da kai ba tare da matashin ya zama mara manufa ba.
Gwagwarwa ya yi kira ga al’ummar Jihar Kano da su bai wa gwamnatin Abba da ta Shugaban ƙasa, Bola Tinubu haɗin kai a wannan manufa ta samar da ci gaba a kowanne fanni. Sannan ya buƙaci al’umma su bai wa shugaban ƙasa haɗin kai ta yadda idan ya yi tazarce za a samu sauƙin samun ci gaba a Nijeriya.















Discussion about this post