Tsohon ma’ajin jam’iyyar APC na ƙasa, Hon. Alhaji Bala Muhammad Gwagwarwa ya bayyana cewa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ƙirƙiri shirin samar da manufar Kano ce ta farko domi sanya wa Kanawa kishin jiharsu ne.
A cewarsa, an samar da shirin ne domin Jihar Kano ta samu ci gaba da ɓata samu ba a baya, sakamakon raba kan jama’a da yadda wasu suke fifita ra’ayinsu a kan Kano, wanda wannan ya sa Gwamna Abba ba tsayu kan manufarsa ta haɗa kan Kanawa domin kowa ya ba da gudummawarsa ta kowana fanni da ya ƙore kamar ilimi, lafiya, noma, kasuwanci da sauransu.
- Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
- Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
- Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
- Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
- Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”
Alhaji Gwagwarwa ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai.
Har ila yau, ya ƙara da cewa Gwamna Abba ya fifita Kano fiye da ra’ayinsa ba kamar yadda wasu magabata suka yi a lokacin mulkinsu ba, wanda shi ya haifar da matsalar wajen ci gaban Kano.
Haka kuma ya ce wannan manufa ce ta sa Gwamna Abba yake aiki wajen gyara tarbiyya da tunanin matasa na kowa ya dogara da kansa ta hanyar bunƙasa sana’o’in dogaro da kai ba tare da matashin ya zama mara manufa ba.
Gwagwarwa ya yi kira ga al’ummar Jihar Kano da su bai wa gwamnatin Abba da ta Shugaban ƙasa, Bola Tinubu haɗin kai a wannan manufa ta samar da ci gaba a kowanne fanni. Sannan ya buƙaci al’umma su bai wa shugaban ƙasa haɗin kai ta yadda idan ya yi tazarce za a samu sauƙin samun ci gaba a Nijeriya.














