ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mazauna Yankin Sun Tsere Bayan Gano Wasiƙar Kawo Hare-haren Ta’addanci a FCT

by Sulaiman
3 months ago
Fct

Mazauna da dama na al’ummomin Kungaboku da Paze a cikin Babban Birnin Tarayya (FCT) sun tsere daga gidajensu bayan wata wasiƙa da ake zargin ‘yan bindiga ne suka rubuta ta bayyana, wadda ke barazanar kai hare-hare a yankin.

 

A cikin wasiƙar da aka ce an samu a cikin littafin wani ɗalibi a wata makaranta mai zaman kanta, ‘yan bindigar sun yi rantsuwa cewa za su kai hari Kungaboku da makwabciyarta Paze domin ramuwar gayya kan kashe kwamandansu.

ADVERTISEMENT
  • Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Birnin Paris
  • Ƙarin Farashin Fetur: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Nemi A Dakatar Da Karɓar Haraji

Za a iya tuna cewa a ranar 7 ga Maris, sojojin Bataliya ta 7, tare da ‘yansanda da ‘yan sa-kai, sun ceto mutane 19 da aka sace.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Wadanda aka ceto, mafi yawansu mazauna Paze da Kungaboku ne, sun samu ‘yanci ne yayin wani hadin gwiwar bincike da aikin ceto da aka gudanar a yankin Gidan Dogo da ke Karamar Hukumar Bwari.

 

A yayin wannan aiki, an ruwaito cewa sojojin sun kashe wani ɗan bindiga, yayin da sauran suka tsere daga wurin da raunukan harbin bindiga da ake zargin sun samu.

 

An kuma ruwaito cewa an gano wasiƙar barazanar ne a cikin littafin rubutun wani ɗalibi a wata makaranta mai zaman kanta da ke Paze, bayan da wani malami ya gano ta yayin da yake duba aikin gida na ɗalibin.

 

Bayan sanarwa mahukunta makarantar, ‘yansanda sun kama ɗalibin, iyayensa, malamin da kuma shugabannin makarantar domin yi musu tambayoyi da bincike, kafin daga bisani aka sake su.

 

Kamfanin Dillancin Labarai na kasa (NAN) ya ruwaito cewa Kungaboku da Paze, wadanda ke kusa da Byazhin, dake cikin Kubwa a Karamar Hukumar Bwari, sun sha fama da hare-haren ‘yan bindiga a ‘yan kwanakin nan.

Fct
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Sin Ta Aika Da Sakon Taya Murna Ga ‘Yan Wasan Kasar Da Suka Halarci Gasar Paralimpics Karo Na 14

Gwamnatin Sin Ta Aika Da Sakon Taya Murna Ga ‘Yan Wasan Kasar Da Suka Halarci Gasar Paralimpics Karo Na 14

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.