ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Aka Ki Karbar Tallafi Daga Kasar Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Amurka

A kwanan baya, gwamnatin kasar Zambia ta sanar da kin karbar tallafin hidimar kiwon lafiya da kasar Amurka ta yi shirin samar mata. Bayan da na karanta wannan labari, na yi mamakin yadda kasar Zambia ta kyale niyya mai kyau da aka nuna mata. Sai dai daga bisani na yi kokarin tara dukkan bayanai dangane da lamarin, sa’an nan na fahimci dalilin da ya sa Zambia daukar wannan mataki. Dalilin dai shi ne Amurka ta riga ta sauya salon tallafinta, kuma niyyarta ba ta kirki ba ce.

Kasar Amurka ta tsara shirin ba da tallafin ne bisa dalilin wai taimakawa kasar Zambia a fannonin tinkarar cutar kanjamau, da zazzabin cizon sauro, da kare lafiyar jikin mata masu juna biyu, da wadanda suka haihu. Sai dai bayan zurfafa shawarwari tsakanin kasashen 2, sai niyya ta hakika ta kasar Amurka ta bayyana:

Na farko, duk da cewa kasar Amurka ta yi shirin ba da tallafin, amma ba ta son kashe kudi da yawa. Saboda haka ta rage kudin tallafin da ta yi alkawarin bayarwa daga dala biliyan 1.5 zuwa dala biliyan 1 da dan wani abu. Kana ta bukaci gwamnatin Zambia, da ta samar da dala miliyan 340 a nata bangare, da ware kudi don samar da albashi ga karin wasu jami’an lafiya dubu 40 da za su gudanar da ayyuka masu nasaba.

ADVERTISEMENT

Na biyu, shi ne kasar Amurka na son tattaro kan bayanai, da harkar tsaro a fannin aikin lafiya na kasar da ta karbi tallafinta. Inda a cikin kundin yarjejeniyar tallafi da ta tsara, kasar Amurka ta nemi samun bayanai masu alaka da lafiyar jama’ar kasar Zambia a kai a kai, cikin shekaru 10 masu zuwa. Kana ta kayyade cewa, kasar Zambia za ta samar mata da bayanan duk wata cutar da ka iya yaduwa a cikin gidanta, cikin shekaru 25 masu zuwa.

Na uku, shi ne Amurka na son ganin yadda tallafin da ta bayar zai haifar da sabuwar moriya, wadda za ta koma aljihunta. An ce, a jajiberin ranar da za a kulla yarjejeniyar ba da tallafin, mataimakin sakataren harkokin waje na kasar Amurka Caleb Orr, ya ziyarci Zambia, inda ya gaya wa shugaba Hakainde Hichilema na kasar cewa, dole ne kasar Zambia ta ba kasar Amurka ikon musamman na samun wasu ma’adinai na kasar, irinsu tagulla, da Cobalt, da dai sauransu, kafin Amurka ta ba Zambia tallafin aikin kiwon lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

La’akari da wannan yarjejeniyar tallafi mai cike da son zuciya, ta yaya kasar Zambia za ta iya yarda da ita? Don haka ba mamaki ganin yadda kasar Zambia ta ce yarjejeniyar ta saba wa moriyarta, kuma ta ki sa hannu a kanta.

Hakika, a nahiyar Afirka, ba kasar Zambia ce kadai ta nuna kin amincewa ga niyyar samar da tallafin aikin lafiya na kasar Amurka ba. Sauran kasashe irinsu Zimbabwe da Kenya, dukkansu sun janye jiki daga shirin karbar tallafi daga kasar Amurka, sakamakon yadda suke damuwa kan niyyar kasar Amurka ta mallakar bayanan lafiyar jikin al’ummunsu, da na wasu cututtuka masu yaduwa.

Dalilin da ya sa salon ba da tallafin lafiya na kasar Amurka ya sauya, shi ne sabuwar manufar kiwon lafiya a duniya da kasar Amurka ta gabatar a watan Satumban bara, wadda ta kasance irin ta “mayar da moriyar kasar Amurka a gaban ta duniya”. Sai dai yadda gwamnatin kasar Amurka take fakewa da maganar tallafin jin kai tana neman biyan bukatunta, ko Amurkawa ma ba za su iya yarda da hakan ba. Ace Robinson, shi ne shugaban kungiyar tabbatar da daidaito a fannin aikin kiwon lafiya na kasar Amurka mai taken “Equity is the Word”, ya kuma gayawa kafofin yada labaru a kwanan baya cewa, tuni gwamnatocin kasashe daban daban suka fara taka tsan-tsan a kokarin magance fadawa cikin tarkon kasar Amurka, na yin musayar wasu abubuwa ba tare da nuna adalci ba, kana a wannan karo za su kara damuwa a kan yadda ake neman keta ikon mulkin kansu. Ya kuma kara da cewa, “Ana kwatar albarkatunsu, ana kuma neman sanya su biyan karin kudi. Tabbas ba za a taba yarda da wannan shiri ba.” (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Cimma Nasarar Manufar Nan Ta Inganta Lafiyar Jama’a A Wa’adin Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Cimma Nasarar Manufar Nan Ta Inganta Lafiyar Jama’a A Wa’adin Shirin Raya Kasa Karo Na 15

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.