ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Aka Ki Karbar Tallafi Daga Kasar Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Amurka

A kwanan baya, gwamnatin kasar Zambia ta sanar da kin karbar tallafin hidimar kiwon lafiya da kasar Amurka ta yi shirin samar mata. Bayan da na karanta wannan labari, na yi mamakin yadda kasar Zambia ta kyale niyya mai kyau da aka nuna mata. Sai dai daga bisani na yi kokarin tara dukkan bayanai dangane da lamarin, sa’an nan na fahimci dalilin da ya sa Zambia daukar wannan mataki. Dalilin dai shi ne Amurka ta riga ta sauya salon tallafinta, kuma niyyarta ba ta kirki ba ce.

Kasar Amurka ta tsara shirin ba da tallafin ne bisa dalilin wai taimakawa kasar Zambia a fannonin tinkarar cutar kanjamau, da zazzabin cizon sauro, da kare lafiyar jikin mata masu juna biyu, da wadanda suka haihu. Sai dai bayan zurfafa shawarwari tsakanin kasashen 2, sai niyya ta hakika ta kasar Amurka ta bayyana:

Na farko, duk da cewa kasar Amurka ta yi shirin ba da tallafin, amma ba ta son kashe kudi da yawa. Saboda haka ta rage kudin tallafin da ta yi alkawarin bayarwa daga dala biliyan 1.5 zuwa dala biliyan 1 da dan wani abu. Kana ta bukaci gwamnatin Zambia, da ta samar da dala miliyan 340 a nata bangare, da ware kudi don samar da albashi ga karin wasu jami’an lafiya dubu 40 da za su gudanar da ayyuka masu nasaba.

ADVERTISEMENT

Na biyu, shi ne kasar Amurka na son tattaro kan bayanai, da harkar tsaro a fannin aikin lafiya na kasar da ta karbi tallafinta. Inda a cikin kundin yarjejeniyar tallafi da ta tsara, kasar Amurka ta nemi samun bayanai masu alaka da lafiyar jama’ar kasar Zambia a kai a kai, cikin shekaru 10 masu zuwa. Kana ta kayyade cewa, kasar Zambia za ta samar mata da bayanan duk wata cutar da ka iya yaduwa a cikin gidanta, cikin shekaru 25 masu zuwa.

Na uku, shi ne Amurka na son ganin yadda tallafin da ta bayar zai haifar da sabuwar moriya, wadda za ta koma aljihunta. An ce, a jajiberin ranar da za a kulla yarjejeniyar ba da tallafin, mataimakin sakataren harkokin waje na kasar Amurka Caleb Orr, ya ziyarci Zambia, inda ya gaya wa shugaba Hakainde Hichilema na kasar cewa, dole ne kasar Zambia ta ba kasar Amurka ikon musamman na samun wasu ma’adinai na kasar, irinsu tagulla, da Cobalt, da dai sauransu, kafin Amurka ta ba Zambia tallafin aikin kiwon lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

La’akari da wannan yarjejeniyar tallafi mai cike da son zuciya, ta yaya kasar Zambia za ta iya yarda da ita? Don haka ba mamaki ganin yadda kasar Zambia ta ce yarjejeniyar ta saba wa moriyarta, kuma ta ki sa hannu a kanta.

Hakika, a nahiyar Afirka, ba kasar Zambia ce kadai ta nuna kin amincewa ga niyyar samar da tallafin aikin lafiya na kasar Amurka ba. Sauran kasashe irinsu Zimbabwe da Kenya, dukkansu sun janye jiki daga shirin karbar tallafi daga kasar Amurka, sakamakon yadda suke damuwa kan niyyar kasar Amurka ta mallakar bayanan lafiyar jikin al’ummunsu, da na wasu cututtuka masu yaduwa.

Dalilin da ya sa salon ba da tallafin lafiya na kasar Amurka ya sauya, shi ne sabuwar manufar kiwon lafiya a duniya da kasar Amurka ta gabatar a watan Satumban bara, wadda ta kasance irin ta “mayar da moriyar kasar Amurka a gaban ta duniya”. Sai dai yadda gwamnatin kasar Amurka take fakewa da maganar tallafin jin kai tana neman biyan bukatunta, ko Amurkawa ma ba za su iya yarda da hakan ba. Ace Robinson, shi ne shugaban kungiyar tabbatar da daidaito a fannin aikin kiwon lafiya na kasar Amurka mai taken “Equity is the Word”, ya kuma gayawa kafofin yada labaru a kwanan baya cewa, tuni gwamnatocin kasashe daban daban suka fara taka tsan-tsan a kokarin magance fadawa cikin tarkon kasar Amurka, na yin musayar wasu abubuwa ba tare da nuna adalci ba, kana a wannan karo za su kara damuwa a kan yadda ake neman keta ikon mulkin kansu. Ya kuma kara da cewa, “Ana kwatar albarkatunsu, ana kuma neman sanya su biyan karin kudi. Tabbas ba za a taba yarda da wannan shiri ba.” (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Cimma Nasarar Manufar Nan Ta Inganta Lafiyar Jama’a A Wa’adin Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Cimma Nasarar Manufar Nan Ta Inganta Lafiyar Jama’a A Wa’adin Shirin Raya Kasa Karo Na 15

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.