ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Yamma Suka Yi Shiru Kan Shirin Japan Na Zubar Da Ruwan Tagwalon Nukiliya a Cikin Teku?

by CMG Hausa
3 years ago
Japan

Kawo ran 10 ga watam Yuli, wato kusan mako guda ke nan bayan da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA a takaice, ta fitar da rahoton game da shirin kasar Japan na zubar da ruwan tagwalon nukiliyara Fukushima a teku. A wannan lokaci, kasashen duniya kamar kasashen tsibiran Pacific, da Philippines, da Indonesia, da Afirka ta Kudu, da Peru, da Sin da Koriya ta Kudu sun nuna fushi sosai ga shirin Japan na zubar da gurbataccen ruwan a teku, amma a bangare nasu, abin da kasashen yamma, kamar kasar Amurka suka yi ya sha bamban kwarai.

Me ya sa wasu kasashen yamma ba su nuna damuwa, har ma sun “kwantar da hankulansu” da shirin Japan din na zubar da gurbataccen ruwan nukiliya a cikin teku ba?

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Harkokin Kudin Amurka Janet Yellen

A cewar jaridar Los Angeles Times, a cikin shekarun 1940 da 1950, Amurka ta gudanar da gwaje-gwajen nukiliya har sau 67 a tsibiran Marshall dake cikin tekun Pacific. Bugu da kari, a baya, Amurka ta taba yin jigilar gurbatacciyar kasar nukiliya da aka samu a wurin gwajin nukiliya dake jihar Nevada zuwa tsibiran Marshall, sannan ta zubar da irin wannan gurbataciyyar kasar nukiliya a tsibirin Marshall kai tsaye. Wannan na iya zama amsar dalilin da ya sa Amurka ta dade da yarda da shirin Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku, domin tana daya daga cikin wadanda suka fara gurbacewar teku.

ADVERTISEMENT

Ban da wannan, a ganin Amurka, batun tsaron nukiliya ya kasance kamar wani abun da ta iya yin musayar moriya. Wasu bayanan nazari sun yi nuni da cewa, bayan karshen yakin duniya na biyu, makamashin nukiliya shi ne makami ne da Amurka take amfani da shi wajen mallakar Japan. A daya bangare kuma, shi wani muhimmin makami ne ga Japan da take jinginawa da kuma dogara da kasar Amurka.

Amurka ta dade tana ikirarin kare “hakkin bil’adam” na daukacin al’umma. Amma a hakika dai, tana kula da mulkin danniya nata kawai, maimakon hakkin bil’adam, kuma tana kula da moriyar siyasa ta radin kanta kawai, maimakon hakkin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Tekun Pacifik teku ne na daukacin bil’adama na duk duniya baki daya. Kamata ya yi gwamnatin Japan ta yi biyayya ga kiraye-kirayen adalci na bangarori daban daban, sannan ta dakatar da shirinta na zubar da gurbataccen ruwan nukiliya a cikin teku nan da nan. Wadancan kasashen yammacin duniya da har yanzu suke shiru, kada su zama abokan hulda na wannan shiri. (Safiyah Ma)

Japan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Next Post
Jami’in Ghana: Ci Gaban Sin A Fannin Noma Da Yaki Da Fatara Na Karfafa Gwiwar Sauran Kasashe Masu Tasowa

Jami’in Ghana: Ci Gaban Sin A Fannin Noma Da Yaki Da Fatara Na Karfafa Gwiwar Sauran Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Japan

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Japan

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.